• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Hallarci Taron Kolin Tattalin Arziki A Paris

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Tinubu Zai Hallarci Taron Kolin Tattalin Arziki A Paris
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tafi kasar waje a karon farko tun bayan da ya karbi ragamar mulki a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.

A ranar Alhamis, 22 ga watan Yunin 2023 ne ake sa ran shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tashi zuwa Paris, babban birnin kasar Faransa, inda zai gana da sauran takwarorinsa na kasashen duniya wadanda ake sa ran za su tattauna kuma su rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeiyar tattalin arzikin duniya wato ‘Global Financial Pact.”

  • An Bai Wa Iyalin ‘Yansandan Da Suka Mutu A Bakin Aiki Cakin 23m A Zamfara
  • Ba Zan Je Saudiyya Ba Ina Nan Daram A Turai — Lukaku

Yarjejeniyar za ta bai wa kasashe masu raunin tattalin arziki fifikon kasancewa kan gaba wajen samun tallafi da kuma zuba jari.

Kasashen da ke cikin wannan rukuni su ne kasashen da suke kan gaba wajen fuskantar matsalolin sauyin yanayi da na makamashi, kana sun kasance kasashen da suka fi jin radadin annobar COVID-19.

Wata sanarwar da daga ofishin mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan ayyuka na musamman, Dele Adeleke, ta bayyana cewa shugaban zai halarci taron kolin na wuni biyu daga ranar Alkhamis zuwa Juma’a, 23 ga watan Yunin 2023.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Ana sa ran taron zai tattauna kan yiwuwar sake duba kasashen da suke fuskantar kalubalen tattalin arziki a gajeren zango, musamman ma wadanda bashi ya yi musu katutu domin samo musu dabarun zamani na tattalin arziki wanda zai taimaka musu wajen tunkarar hatsarin matsalolin sauyin yanayi.

Kazalika, taron zai mai da hanakali wajen inganta ci gaban kasashen da suke samun karancin kudaden shiga, kana ya karfafa zuba jari a fannin makamashi mai tsafta musamman domin yunkurin da duniya take yi na sauya amfani da makamashi mai tsafta domin kasashe masu tasowa.

Sanarawar ta kuma bayyana cewa, shugaba Tinubu da sauran shugabannin kasashen duniya, manyan kamfanoni, masana harkar kudi da kwararru a sha’anin tattalin arziki za su yi duba na tsanaki a kan farfado da komadar tattalin arzikin kasashe daga radadin annobar COVID-19 da karuwar matsalar talauci, tare da zummar samar da damar samun kudade da kofar zuba jari wanda zai haifar da ci gaba mai dorewa.

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ne zai kasance mai masaukin baki a taron wanda za’a gudanar a Palais Brongniart.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa Tinubu zai samu rakiyar mambobin majalisar shugaban kasa masu ba da shawara a kan dokokin kasa da kuma manyan jami’an gwamnati.

Ana sa ran Tinubu ya dawo gida Nijeriya a ranar Asabar, 24 ga watan Yuni bayan kammala taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FaransaParisTaron Tattalin ArzikiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bai Wa Iyalin ‘Yansandan Da Suka Mutu A Bakin Aiki Cakin 23m A Zamfara

Next Post

Abubakar Y. Sulaiman Ya Sake Zama Kakakin Majalisar Dokokin Bauchi

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

7 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

9 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

10 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

10 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

14 hours ago
Next Post
Abubakar Y. Sulaiman Ya Sake Zama Kakakin Majalisar Dokokin Bauchi

Abubakar Y. Sulaiman Ya Sake Zama Kakakin Majalisar Dokokin Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.