ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Hallarci Taron Kolin Tattalin Arziki A Paris

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tafi kasar waje a karon farko tun bayan da ya karbi ragamar mulki a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.

A ranar Alhamis, 22 ga watan Yunin 2023 ne ake sa ran shugaba Bola Ahmed Tinubu zai tashi zuwa Paris, babban birnin kasar Faransa, inda zai gana da sauran takwarorinsa na kasashen duniya wadanda ake sa ran za su tattauna kuma su rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeiyar tattalin arzikin duniya wato ‘Global Financial Pact.”

  • An Bai Wa Iyalin ‘Yansandan Da Suka Mutu A Bakin Aiki Cakin 23m A Zamfara
  • Ba Zan Je Saudiyya Ba Ina Nan Daram A Turai — Lukaku

Yarjejeniyar za ta bai wa kasashe masu raunin tattalin arziki fifikon kasancewa kan gaba wajen samun tallafi da kuma zuba jari.

ADVERTISEMENT

Kasashen da ke cikin wannan rukuni su ne kasashen da suke kan gaba wajen fuskantar matsalolin sauyin yanayi da na makamashi, kana sun kasance kasashen da suka fi jin radadin annobar COVID-19.

Wata sanarwar da daga ofishin mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan ayyuka na musamman, Dele Adeleke, ta bayyana cewa shugaban zai halarci taron kolin na wuni biyu daga ranar Alkhamis zuwa Juma’a, 23 ga watan Yunin 2023.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ana sa ran taron zai tattauna kan yiwuwar sake duba kasashen da suke fuskantar kalubalen tattalin arziki a gajeren zango, musamman ma wadanda bashi ya yi musu katutu domin samo musu dabarun zamani na tattalin arziki wanda zai taimaka musu wajen tunkarar hatsarin matsalolin sauyin yanayi.

Kazalika, taron zai mai da hanakali wajen inganta ci gaban kasashen da suke samun karancin kudaden shiga, kana ya karfafa zuba jari a fannin makamashi mai tsafta musamman domin yunkurin da duniya take yi na sauya amfani da makamashi mai tsafta domin kasashe masu tasowa.

Sanarawar ta kuma bayyana cewa, shugaba Tinubu da sauran shugabannin kasashen duniya, manyan kamfanoni, masana harkar kudi da kwararru a sha’anin tattalin arziki za su yi duba na tsanaki a kan farfado da komadar tattalin arzikin kasashe daga radadin annobar COVID-19 da karuwar matsalar talauci, tare da zummar samar da damar samun kudade da kofar zuba jari wanda zai haifar da ci gaba mai dorewa.

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ne zai kasance mai masaukin baki a taron wanda za’a gudanar a Palais Brongniart.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa Tinubu zai samu rakiyar mambobin majalisar shugaban kasa masu ba da shawara a kan dokokin kasa da kuma manyan jami’an gwamnati.

Ana sa ran Tinubu ya dawo gida Nijeriya a ranar Asabar, 24 ga watan Yuni bayan kammala taron.

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Abubakar Y. Sulaiman Ya Sake Zama Kakakin Majalisar Dokokin Bauchi

Abubakar Y. Sulaiman Ya Sake Zama Kakakin Majalisar Dokokin Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.