• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Shugaban Tarayyar Sobiet Mikhail Gorbacheb Ya Rasu

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Labarai
0
Tsohon Shugaban Tarayyar Sobiet Mikhail Gorbacheb Ya Rasu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Tarayyar Sobiet na karshe Mikhail Gorbacheb, ya mutu yana da shekara 91. Mista Gorbacheb, wanda ya karbi ragamar mulki a 1985, ya yi fice wajen bude kofofin tsohuwar Tarrayar Sobiet da kuma kusancinsa da kasashen Yamma, amma ya kasa hana kasarsa rugujewa a 1991.

‘Yan kasar Rasha da dama sun dora alhakin rugujewar Tarrayar Sobiet a kan manufofinsa na kawo sauyi. Jami’an asibitin da ya mutu sun ce ya yi fama da doguwar rashin lafiya. Shugaban kasar Rasha, Bladimir Putin, ya bayyana alhininsa game da mutuwar Mista Gorbacheb, kamar yadda mai magana da yawunsa Dmitry Peskob ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Rasha Interfad a cewar Reuters.

  • Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma
  • …Dalla-dallar Yadda Aka Kashe Kudin Tallafin Mai

Mista Gorbacheb ya zama babban sakataren jam’iyyar gurguzu ta tsohuwar Tarayyar Sobiet da kuma shugaban kasa yana da shekara 54.

A wancan lokaci shi ne mamba mafi karancin shekaru a majalisar da ke mulki da aka fi sani da Politburo, kuma ana kallonsa a matsayin matashi mai kwarjini, bayan shekarun da aka shafe ana samun shugabannin da suka tsufa.

Manufarsa ta bai wa al’ummar kasar damar bayyana ra’ayoyinsu ciki har da sukar gwamnati wanda wani abu ne mai wuya a baya. Sai dai ta sa yankuna da dama sun fara neman ‘yancin kai, wanda a karshe ya kai ga rugujewarta.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

A matakin kasa da kasa ya cimma yarjejeniyar takaita amfani da makamai tsakanin kasarsa da Amurka, kuma ya ki shiga tsakani a lokacin da kasashen gabashin Turai suka yi wa shugabanninsu masu ra’ayin gurguzu bore.

Kasashen yammacin duniya na kallonsa a matsayin wanda ya jagoranci yadda za a kawo karshen yakin cacar[1]baka.

An ba shi lambar yabo ta zaman lafiya ta Nobel a shekara ta 1990, saboda rawar da ya taka wajen kawo sauye[1]sauye a dangantakar da ke tsakanin kasashen Gabashi da na Yamma.

Sai dai a sabuwar Rashar da ta bayyana bayan 1991, ya nesanta kansa daga harkar siyasa inda ya mayar da hankali a kan ilimi da ayyukan jin kai.

Ya yi yunkurin komawa fagen siyasa a 1996, amma kashi 0.5 na kur’iun da aka kada ne ya samu a zaben shugaban kasa. A shekarun baya-bayan nan ya rika fama da rashin lafiya kuma an rika jinyarsa a asibiti.

Kamfanin dillancin labarai na Tass ya ce za a binne shi a makabartar Nobodebichy da ke birnin Moscow, inda a nan ne ake binne fitattun ‘yan kasar, kusa da matarsa Raisa wadda ta mutu a 1999.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: RashaRasuwaShugabaSobiet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Next Post

Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

Related

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

12 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

13 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

14 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

15 hours ago
Next Post
Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.