• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsoron Tashin Bom: ‘Yan Sanda Sun Hana Motoci Shiga Duk Wani Filin Sallar Idi Da Ke Abuja

by Muhammad
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Mutum 25 Ne Suka Bace Cikin Wata 6 A Jihar Abia — ‘Yan Sanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan harin da aka kai a gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja da kuma bayanan sirri kan harin da aka shirya kai wa a harabar filin sallar idi a ranar Asabar din 2022, rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja ta haramtawa motoci shiga duk wani filin sallar idi da ke Abuja.

Kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya, CP Babaji Sunday, ne ya bayyana hakan a cikin sakonsa na Sallah ga mazauna babban birnin tarayya Abuja.

  • Hukumar Gidan Gyara-hali Ta Nijeriya Ta Tabbatar Da Harin Gidan Yarin Kuje, Abuja
  • Wani Abun Fashe Wa Da Ake Zaton Bom Ne Ya Tashi A Gidan Yarin Kuje Da Ke Abuja

Kwamishinan ya kuma kara da cewa, a kokarin cimma matsaya guda na tabbatar da tsaro, rundunar za ta kara tsaurara matakan tsaro da ayyukanta na bincike.

Jami’an ‘yan sanda da ke sa ido kan wuraren ibada, wuraren shakatawa da wuraren zaman Jama’a da kuma mayar da martani cikin gaggawa. ga duk wani kira na damuwa daga ko’ina cikin Abuja.

Wani bangare na sanarwar mai dauke da sa hannun mai magana da yawun rundunar, DSP Josephine Adeh, ta ce, “Musulmin da za su so gudanar da Sallar Idi a filin Sallar Idi na kasa da ke kan titin filin jirgin, su lura cewa akwai isasshen fili da aka ware, ana kira da Jama’a da su guji yin Sallah a kan titin mota domin tabbatar da tsari da tafiyar da zirga-zirga yadda ya kamata, haka nan kuma za a ringa faka ababen hawa a gadar Dantata daga karfe 7:00 -10:00 na safe.

Labarai Masu Nasaba

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

“A cikin haka motocin banza ba za a bari su yi fakin a gaban filin sallah ba a kan titin mota.

“A duk sauran wuraren da ake yin addu’o’in da ke cikin babban birnin tarayya Abuja, babu wata mota da za a ba da izinin yin fakin tazarar mita 200 a kusa da filin sallah. Don haka ana shawartar masu ibada da mazauna wurin da su ba jami’an ‘yan sanda da aka tura hadin kai don aiwatar da su.”

CP ya kara da cewa, an yi amfani da dabara da kuma kadarori na rundunar ta hanyar dabara a cikin lunguna da sako na yankin domin dakile duk wani laifi ko barazana ga rayukan mazauna yankin.

Hakazalika ya nanata kudurin rundunar na yin aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro da kuma ‘yan kasa wajen inganta tsaron jama’a, zaman lafiya da tsaro a babban birnin tarayya Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Faransa

Next Post

Lokutan Sallar Idi A Wasu Masallatan Idi Da ke Cikin Birnin Kano

Related

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

3 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

4 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

16 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

19 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

1 day ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

1 day ago
Next Post
Lokutan Sallar Idi A Wasu Masallatan Idi Da ke Cikin Birnin Kano

Lokutan Sallar Idi A Wasu Masallatan Idi Da ke Cikin Birnin Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Tsoron

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.