ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsoron Tashin Bom: ‘Yan Sanda Sun Hana Motoci Shiga Duk Wani Filin Sallar Idi Da Ke Abuja

by Muhammad
3 years ago
Tsoron

Biyo bayan harin da aka kai a gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja da kuma bayanan sirri kan harin da aka shirya kai wa a harabar filin sallar idi a ranar Asabar din 2022, rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja ta haramtawa motoci shiga duk wani filin sallar idi da ke Abuja.

Kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya, CP Babaji Sunday, ne ya bayyana hakan a cikin sakonsa na Sallah ga mazauna babban birnin tarayya Abuja.

  • Hukumar Gidan Gyara-hali Ta Nijeriya Ta Tabbatar Da Harin Gidan Yarin Kuje, Abuja
  • Wani Abun Fashe Wa Da Ake Zaton Bom Ne Ya Tashi A Gidan Yarin Kuje Da Ke Abuja

Kwamishinan ya kuma kara da cewa, a kokarin cimma matsaya guda na tabbatar da tsaro, rundunar za ta kara tsaurara matakan tsaro da ayyukanta na bincike.

ADVERTISEMENT

Jami’an ‘yan sanda da ke sa ido kan wuraren ibada, wuraren shakatawa da wuraren zaman Jama’a da kuma mayar da martani cikin gaggawa. ga duk wani kira na damuwa daga ko’ina cikin Abuja.

Wani bangare na sanarwar mai dauke da sa hannun mai magana da yawun rundunar, DSP Josephine Adeh, ta ce, “Musulmin da za su so gudanar da Sallar Idi a filin Sallar Idi na kasa da ke kan titin filin jirgin, su lura cewa akwai isasshen fili da aka ware, ana kira da Jama’a da su guji yin Sallah a kan titin mota domin tabbatar da tsari da tafiyar da zirga-zirga yadda ya kamata, haka nan kuma za a ringa faka ababen hawa a gadar Dantata daga karfe 7:00 -10:00 na safe.

LABARAI MASU NASABA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

“A cikin haka motocin banza ba za a bari su yi fakin a gaban filin sallah ba a kan titin mota.

“A duk sauran wuraren da ake yin addu’o’in da ke cikin babban birnin tarayya Abuja, babu wata mota da za a ba da izinin yin fakin tazarar mita 200 a kusa da filin sallah. Don haka ana shawartar masu ibada da mazauna wurin da su ba jami’an ‘yan sanda da aka tura hadin kai don aiwatar da su.”

CP ya kara da cewa, an yi amfani da dabara da kuma kadarori na rundunar ta hanyar dabara a cikin lunguna da sako na yankin domin dakile duk wani laifi ko barazana ga rayukan mazauna yankin.

Hakazalika ya nanata kudurin rundunar na yin aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro da kuma ‘yan kasa wajen inganta tsaron jama’a, zaman lafiya da tsaro a babban birnin tarayya Abuja.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola
Manyan Labarai

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa
Manyan Labarai

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Next Post
Lokutan Sallar Idi A Wasu Masallatan Idi Da ke Cikin Birnin Kano

Lokutan Sallar Idi A Wasu Masallatan Idi Da ke Cikin Birnin Kano

LABARAI MASU NASABA

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.