ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsoron Tashin Bom: ‘Yan Sanda Sun Hana Motoci Shiga Duk Wani Filin Sallar Idi Da Ke Abuja

by Muhammad
4 years ago
Tsoron

Biyo bayan harin da aka kai a gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja da kuma bayanan sirri kan harin da aka shirya kai wa a harabar filin sallar idi a ranar Asabar din 2022, rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja ta haramtawa motoci shiga duk wani filin sallar idi da ke Abuja.

Kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya, CP Babaji Sunday, ne ya bayyana hakan a cikin sakonsa na Sallah ga mazauna babban birnin tarayya Abuja.

  • Hukumar Gidan Gyara-hali Ta Nijeriya Ta Tabbatar Da Harin Gidan Yarin Kuje, Abuja
  • Wani Abun Fashe Wa Da Ake Zaton Bom Ne Ya Tashi A Gidan Yarin Kuje Da Ke Abuja

Kwamishinan ya kuma kara da cewa, a kokarin cimma matsaya guda na tabbatar da tsaro, rundunar za ta kara tsaurara matakan tsaro da ayyukanta na bincike.

ADVERTISEMENT

Jami’an ‘yan sanda da ke sa ido kan wuraren ibada, wuraren shakatawa da wuraren zaman Jama’a da kuma mayar da martani cikin gaggawa. ga duk wani kira na damuwa daga ko’ina cikin Abuja.

Wani bangare na sanarwar mai dauke da sa hannun mai magana da yawun rundunar, DSP Josephine Adeh, ta ce, “Musulmin da za su so gudanar da Sallar Idi a filin Sallar Idi na kasa da ke kan titin filin jirgin, su lura cewa akwai isasshen fili da aka ware, ana kira da Jama’a da su guji yin Sallah a kan titin mota domin tabbatar da tsari da tafiyar da zirga-zirga yadda ya kamata, haka nan kuma za a ringa faka ababen hawa a gadar Dantata daga karfe 7:00 -10:00 na safe.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“A cikin haka motocin banza ba za a bari su yi fakin a gaban filin sallah ba a kan titin mota.

“A duk sauran wuraren da ake yin addu’o’in da ke cikin babban birnin tarayya Abuja, babu wata mota da za a ba da izinin yin fakin tazarar mita 200 a kusa da filin sallah. Don haka ana shawartar masu ibada da mazauna wurin da su ba jami’an ‘yan sanda da aka tura hadin kai don aiwatar da su.”

CP ya kara da cewa, an yi amfani da dabara da kuma kadarori na rundunar ta hanyar dabara a cikin lunguna da sako na yankin domin dakile duk wani laifi ko barazana ga rayukan mazauna yankin.

Hakazalika ya nanata kudurin rundunar na yin aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro da kuma ‘yan kasa wajen inganta tsaron jama’a, zaman lafiya da tsaro a babban birnin tarayya Abuja.

Tsoron
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Lokutan Sallar Idi A Wasu Masallatan Idi Da ke Cikin Birnin Kano

Lokutan Sallar Idi A Wasu Masallatan Idi Da ke Cikin Birnin Kano

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.