• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani mahaifi mai shekaru 60 mai suna Malam Danjuma da ɗansa Ibrahim Danjuma mai shekaru 35 da kuma Aminu Gaye mai shekaru 35 sun rasa rayukansu yayin ciro wata waya da ta fada masai a kauyen ‘Yar Gwanda da ke karamar hukumar Tsanyawa a Jihar Kano.

Rahotanni sun bayyana cewar mutanen uku sun makale ne a cikin ramin wata masai yayin da suke kokarin dauko wayar da ta fada ciki a ranar Lahadi.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 A Kasuwa A Zamfara
  • Tsaro: Nijeriya Za Ta Karbo Jiragen Yaki 24 Daga Kasar Italiya

Kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Abdullahi, ya tabbatar wa LEADERSHIP faruwar lamarin a ranar Litinin.

Ya ce an ceto Alasan da ransa, yayin da sauran ukun kuma aka ceto su a sume amma daga baya aka tabbatar da mutuwarsu a wani asibiti da ke Bichi.

A cewar Abdullahi, a ranar Lahadi 21 ga watan Afrilu, 2024, hukumar ta samu kiran agaji da misalin karfe 11:00 na safe daga wani Aminu Yar Gwanda, wanda ya sanar da faruwar lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Ya ce a lokacin da suka isa wajen, sun tarar da wani Malam Danjuma, mai shekaru 60 ya shiga cikin ramin domin ya ciro wayarsa da ta fada ciki amma ya kasa fitowa.

Ɗansa Ibrahim Danjuma mai shekaru 35, shi ma ya shiga ramin da nufin ceto mahaifinsa amma dukkaninsu suka makale.

Abdullahi, ya kara da cewa mutum na uku, Aminu T Gaye mai shekaru 35, wanda ya yi kokarin ceto su amma ya kasa, kazalika mutum na hudu Abbas Alasan mai shekaru 28 shi ma ya kasa ceto su.

Amma ya ce mutane uku da aka ceto an mika su ga jami’in ‘yansanda na shiyyar Tsanyawa.

Jami’in dan sandan da ya garzaya da su asibiti a Bichi, SP Iro Lado, ya tabbatar da mutuwar mutanen ukun, amma ya ce mutum na hudun na raye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ƊakanoMasaiRamiUba
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 A Kasuwa A Zamfara

Next Post

Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

50 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

2 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

3 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

4 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

16 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

16 hours ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya

Yanzu-Yanzu: Jami'an Tsaro Sun Cafke Jami'in Binance A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.