• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Uba Da Ɗa Sun Mutu Wajen Ciro Waya A Masai A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani mahaifi mai shekaru 60 mai suna Malam Danjuma da ɗansa Ibrahim Danjuma mai shekaru 35 da kuma Aminu Gaye mai shekaru 35 sun rasa rayukansu yayin ciro wata waya da ta fada masai a kauyen ‘Yar Gwanda da ke karamar hukumar Tsanyawa a Jihar Kano.

Rahotanni sun bayyana cewar mutanen uku sun makale ne a cikin ramin wata masai yayin da suke kokarin dauko wayar da ta fada ciki a ranar Lahadi.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 A Kasuwa A Zamfara
  • Tsaro: Nijeriya Za Ta Karbo Jiragen Yaki 24 Daga Kasar Italiya

Kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Abdullahi, ya tabbatar wa LEADERSHIP faruwar lamarin a ranar Litinin.

Ya ce an ceto Alasan da ransa, yayin da sauran ukun kuma aka ceto su a sume amma daga baya aka tabbatar da mutuwarsu a wani asibiti da ke Bichi.

A cewar Abdullahi, a ranar Lahadi 21 ga watan Afrilu, 2024, hukumar ta samu kiran agaji da misalin karfe 11:00 na safe daga wani Aminu Yar Gwanda, wanda ya sanar da faruwar lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

Ya ce a lokacin da suka isa wajen, sun tarar da wani Malam Danjuma, mai shekaru 60 ya shiga cikin ramin domin ya ciro wayarsa da ta fada ciki amma ya kasa fitowa.

Ɗansa Ibrahim Danjuma mai shekaru 35, shi ma ya shiga ramin da nufin ceto mahaifinsa amma dukkaninsu suka makale.

Abdullahi, ya kara da cewa mutum na uku, Aminu T Gaye mai shekaru 35, wanda ya yi kokarin ceto su amma ya kasa, kazalika mutum na hudu Abbas Alasan mai shekaru 28 shi ma ya kasa ceto su.

Amma ya ce mutane uku da aka ceto an mika su ga jami’in ‘yansanda na shiyyar Tsanyawa.

Jami’in dan sandan da ya garzaya da su asibiti a Bichi, SP Iro Lado, ya tabbatar da mutuwar mutanen ukun, amma ya ce mutum na hudun na raye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ƊakanoMasaiRamiUba
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 A Kasuwa A Zamfara

Next Post

Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya

Related

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

12 minutes ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

53 minutes ago
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

1 hour ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

5 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

7 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

19 hours ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Jami’an Tsaro Sun Cafke Jami’in Binance A Kenya

Yanzu-Yanzu: Jami'an Tsaro Sun Cafke Jami'in Binance A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.