• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wa’adin da Shugaba Kasa Bola Ahmad Tinubu, ya bai wa hukumomin tsaro na su karbo bashin Naira tirilayan 1.1, wanda Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ba wa manoman shinkafa a karkashin shirin aikin noma na ‘Anchor Borrowers’, ya cika, amma shiru ka ke ji har yanzu wadannan manoma ba su maido kudaden ba.

Idan za a iya tunawa, Shugaba Tinubun ya umarci hukumomin su karbo wadannan zunzurutun kudade kafin ranar 18 ga watan Satumbar 2023 da muke ciki.

  • Xi Ya Karfafawa ‘Ya‘yan Wadanda Suka Sadaukar Da Rayuwarsu Da Su Zama Amintattu Masu Kare JKS Da Al’umma
  • Kaunar Da Xi Jinping Yake Nuna Wa Gari, Dangi Da Kuma Al’ummar Kasa

An bayar da wannan bashi ne domin kokarin sake habaka harkokin noma a Nijeriya tun a shekarar 2018. Koda-yake dai shirin ya samu nasarori a wasu daga cikin jihohin wannan kasa, inda kuma ya samu tasgaro a wasu jihohin sakamakon kin biyan bashin da wasu daga cikin manoman shinkafar da suka amfana suka yi.

Kazalika, an yi zargin cewa wasu daga cikin jami’an da aka dora wa nauyin bayar da bashin, sun karkatar da wani kaso daga cikin kudaden domin amfanin kawunansu.

Daga cikin wannnan adadi na Naira Tiriliyan 1.1 da aka bai wa  Manoman  Shinkafar, Naira biliyan 546 kacal aka iya maido wa. Amma, bisa wannan umarni da Shugaban Kasar ya bayar ne, ake sa ran manoman da suka ki biyan wadannan kudade da kuma sauran jami’an da aka dorawa nauyin karbo bashisshikan, suka karkatar da wani kaso daga ciki, za su maido da sama da Naira biliyan 577.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Bugu da kari, wannan ya hada daruruwan manoman shinkafar da suka yi rijista da kungiyoyi aka ba su wannan rance, da ya hada da kayan aikin noma kamar takin zamani, magungunan feshi da sauransu.

Ana sa ran kuma manoman za su biya bashin ta hanyar bayar da wani bangare na amfanin da  suka girbe ko kuma ta hanyar biya da kudi lakadan.

Sai dai, karbo wannna bashi ya zamo wa Babban Bankin CBN wani babban kalubale ganin cewa, duk iya kokarin da aka yi na karbo bashin ta hanyar kungiyoyin manoman shinkafar, amma hakansu bai cimma ruwa ba.

Har ila yau, domin cika wannan umarni na Shugaba Tinubu, kungiyar manoman shinkafa ta kasa (RIFAN), ta fitar da wata takarda mai dauke da kwanan watan 30 ga watan Agustan 2023, inda ta umarci kafatanin rassan kungiyoyinta na jihohi da su yi aiki tare da jami’an tsaro domin karbo wannan bashi.

Sai dai, tun bayan wannan umarnin na RIFAN, Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, bashin da aka karbo daga gun manoman da suka amfana a jihohin, bai taka kara ya karya ba.

Haka zalika, dalilan da suka janyo tarnaki wajen karbo wadannan bashisshika, kamar yadda Mataimakin Sakatare Janar na RIFAN din reshen Jihar Kano, Malam Ado Hassan, ya shelanta suna da daman gaske.

Hassan ya kara da cewa, kungiyar reshen jihar ta karbi bashin na kimanin Naira biliyan 12 daga 2017 zuwa  2020, amma bashin da ta iya karbo wa daga wurin wadannan manoma da suka amfana, bai wuce kaso 30 a cikin 100.

Sannan ya yi ikirarin cewa, a kakar noma ta 2018 ‘ya’yan kungiyar reshen jihar,  manoman shinkafa 44, 807 ne suka amfana a karkashin wannan shiri, duk kuwa da cewa sun fuskanci mummunar ambaliayar ruwan sama a wannan shekarar.

Ya ci gaba da cewa, a 2019 an fuskanci kalubalen Annobar Korona, wadda ba manoman shinkafa kadai ta shafa ba har da hada-hadar kasuwanci a fadin duniya baki-daya.

Sannan ya sake kokawa kan cewa, manoman shinkafar ba su samu wata diyya a kan asarar da suka yi ba, bayan afkuwar wannan annoba tare da kuma ta ambaliyar ruwan sama daga wurin Kamfanin Inshorar Aikin Noma na kasa (NAIC) ba.

Kazalika ya ce, a kungiyance an kai wannan rahoto kan afkuwar wannan annoba guda biyu, koda-yake an turo  Jami’an CBN da  na NAIC, zuwa gonakan manoman domin tantance asarar da suka tabka, amma shiru kake ji babu wani agaji ko tallafi da aka kawo musu.

Sannan sun bi hanyoyi da dama don karbo bashi, ciki har da yin amfani da sarakunan gargakiya, kotuna da sauran dabaru daban-daban, amma abin ya faskara.

Har ila yau, wani manomin shinkafa a Jihar Kano, Alhaji Ahmadu Usman ya yi nuni da cewa, zai wuya a iya karbo wadannan basussuka, domin kuwa ba hakikanin manoman da suka dace aka baiwa bashin ba, ‘yan siyasa aka bai wa suka yi san ransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wace Irin Asara Girgizar Kasa Ta Haifar A Maroko?

Next Post

Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

4 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

11 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Tinubu

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.