• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wa’adin da Shugaba Kasa Bola Ahmad Tinubu, ya bai wa hukumomin tsaro na su karbo bashin Naira tirilayan 1.1, wanda Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ba wa manoman shinkafa a karkashin shirin aikin noma na ‘Anchor Borrowers’, ya cika, amma shiru ka ke ji har yanzu wadannan manoma ba su maido kudaden ba.

Idan za a iya tunawa, Shugaba Tinubun ya umarci hukumomin su karbo wadannan zunzurutun kudade kafin ranar 18 ga watan Satumbar 2023 da muke ciki.

  • Xi Ya Karfafawa ‘Ya‘yan Wadanda Suka Sadaukar Da Rayuwarsu Da Su Zama Amintattu Masu Kare JKS Da Al’umma
  • Kaunar Da Xi Jinping Yake Nuna Wa Gari, Dangi Da Kuma Al’ummar Kasa

An bayar da wannan bashi ne domin kokarin sake habaka harkokin noma a Nijeriya tun a shekarar 2018. Koda-yake dai shirin ya samu nasarori a wasu daga cikin jihohin wannan kasa, inda kuma ya samu tasgaro a wasu jihohin sakamakon kin biyan bashin da wasu daga cikin manoman shinkafar da suka amfana suka yi.

Kazalika, an yi zargin cewa wasu daga cikin jami’an da aka dora wa nauyin bayar da bashin, sun karkatar da wani kaso daga cikin kudaden domin amfanin kawunansu.

Daga cikin wannnan adadi na Naira Tiriliyan 1.1 da aka bai wa  Manoman  Shinkafar, Naira biliyan 546 kacal aka iya maido wa. Amma, bisa wannan umarni da Shugaban Kasar ya bayar ne, ake sa ran manoman da suka ki biyan wadannan kudade da kuma sauran jami’an da aka dorawa nauyin karbo bashisshikan, suka karkatar da wani kaso daga ciki, za su maido da sama da Naira biliyan 577.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Bugu da kari, wannan ya hada daruruwan manoman shinkafar da suka yi rijista da kungiyoyi aka ba su wannan rance, da ya hada da kayan aikin noma kamar takin zamani, magungunan feshi da sauransu.

Ana sa ran kuma manoman za su biya bashin ta hanyar bayar da wani bangare na amfanin da  suka girbe ko kuma ta hanyar biya da kudi lakadan.

Sai dai, karbo wannna bashi ya zamo wa Babban Bankin CBN wani babban kalubale ganin cewa, duk iya kokarin da aka yi na karbo bashin ta hanyar kungiyoyin manoman shinkafar, amma hakansu bai cimma ruwa ba.

Har ila yau, domin cika wannan umarni na Shugaba Tinubu, kungiyar manoman shinkafa ta kasa (RIFAN), ta fitar da wata takarda mai dauke da kwanan watan 30 ga watan Agustan 2023, inda ta umarci kafatanin rassan kungiyoyinta na jihohi da su yi aiki tare da jami’an tsaro domin karbo wannan bashi.

Sai dai, tun bayan wannan umarnin na RIFAN, Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, bashin da aka karbo daga gun manoman da suka amfana a jihohin, bai taka kara ya karya ba.

Haka zalika, dalilan da suka janyo tarnaki wajen karbo wadannan bashisshika, kamar yadda Mataimakin Sakatare Janar na RIFAN din reshen Jihar Kano, Malam Ado Hassan, ya shelanta suna da daman gaske.

Hassan ya kara da cewa, kungiyar reshen jihar ta karbi bashin na kimanin Naira biliyan 12 daga 2017 zuwa  2020, amma bashin da ta iya karbo wa daga wurin wadannan manoma da suka amfana, bai wuce kaso 30 a cikin 100.

Sannan ya yi ikirarin cewa, a kakar noma ta 2018 ‘ya’yan kungiyar reshen jihar,  manoman shinkafa 44, 807 ne suka amfana a karkashin wannan shiri, duk kuwa da cewa sun fuskanci mummunar ambaliayar ruwan sama a wannan shekarar.

Ya ci gaba da cewa, a 2019 an fuskanci kalubalen Annobar Korona, wadda ba manoman shinkafa kadai ta shafa ba har da hada-hadar kasuwanci a fadin duniya baki-daya.

Sannan ya sake kokawa kan cewa, manoman shinkafar ba su samu wata diyya a kan asarar da suka yi ba, bayan afkuwar wannan annoba tare da kuma ta ambaliyar ruwan sama daga wurin Kamfanin Inshorar Aikin Noma na kasa (NAIC) ba.

Kazalika ya ce, a kungiyance an kai wannan rahoto kan afkuwar wannan annoba guda biyu, koda-yake an turo  Jami’an CBN da  na NAIC, zuwa gonakan manoman domin tantance asarar da suka tabka, amma shiru kake ji babu wani agaji ko tallafi da aka kawo musu.

Sannan sun bi hanyoyi da dama don karbo bashi, ciki har da yin amfani da sarakunan gargakiya, kotuna da sauran dabaru daban-daban, amma abin ya faskara.

Har ila yau, wani manomin shinkafa a Jihar Kano, Alhaji Ahmadu Usman ya yi nuni da cewa, zai wuya a iya karbo wadannan basussuka, domin kuwa ba hakikanin manoman da suka dace aka baiwa bashin ba, ‘yan siyasa aka bai wa suka yi san ransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wace Irin Asara Girgizar Kasa Ta Haifar A Maroko?

Next Post

Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

2 days ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Next Post
Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

Kungiyoyin CONESAM Sun Baje Kolin Fasahar Sarrafa Kayan Amfanin Gona

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.