• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadatar Abinci: Mun Zuba Naira Biliyan 309 Cikin Shekara 1 A Fannin Noma – Ministan Gona

by Abubakar Abba
12 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya bayyana cewa, a shekarar da ta gabata, Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu, ta zuba zunzurutun kudi kiminin Naira biliyan 309 a fannin aikin noma; domin samar da wadataccen abinci a Nijeriya.

Kyari, ya sanar da hakan ne; a matsayin guda daga cikin nasarorin da ma’aikatarsa ta samu a cikin shekara daya, wanda har ila yau kuma yake nuna nasarar da Shugaba Tinubu ya samu a zangonsa na shekara daya.

  • Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwalejin Noma Da Duba Aikin Babban Asibitin Maradun
  • Sanata Saliu Ya Raba Taki Da Injinan Ban Ruwa Ga Manoman Kwara

Ya ce, kokarin da ake yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki, gwamnatin tarayya ta kaddamar da aikin noman rani; wanda aka noma Alkama a kadada 118,657 da suke a jihohin wannan kasa sha biyar, musamman don noman da zai dauki har tsawon zagayowar wata shekarar.

Ministan ya kara da cewa, gwamnatin ta kuma rabar da tan 58,500 na Shinkafa a daukacin jihohin wannan kasa, ciki har da Abuja da nufin karya farashinta tare kuma da rabar da sauran kayayyakin abinci masu dauke da sinadarin ‘Bitamin A’.

Kyari ya ci gaba da cewa, a kokkarin dakile hauhawar farashin kayan abinci, gwamnatin ta kuma rabar da tan 60,432 na ingantaccen Irin noma kimanin tan 887,255.
”Gwamnatin ta kuma rabar da buhunhunan takin gargajiya kimanin 62,328, da kuma kayan aikin noma ga manoma a wannan fannin na noma, domin samun riba tare da kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

“Domin a samar da ingantaccen tsaro a gonakin manoma, an kara wa jami’an ‘yan sa kai da ke bayar da tsaro a wadannan gonaki na manoma, wato wadanda ake kira a turance ‘agro rangers’ da kuma sauran jami’an tsaron da ke aikin bayar da tsaro a gonakin kudade”, a cewar Kyari.

Kazalika Ministan ya bayyana cewa, gwamnati ta yi matukar kokari wajen bunkasa fannin kiwo da kula da lafiyar dabbobi tare kuma da kara karfafa gudanar da yin bincike a fannin kiwo da sauran ayyukan da suka shafi fannin kiwon.

Haka zalika a cewar tasa, gwamnati ta kara kaimi kwarai da gaske a wannan fanni na noma tare kuma da sarrafa Waken Soya, Kantu, Citta, Zobo da sauran kayayyakin amfanin gona, don a rika fitar da su kasashen waje ana sayarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zimbabwe Ta Yaba Da Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Bangaren Makamashi Mai Tsafta Na Kasar

Next Post

Sin Na Fatan Amurka Na Yin Wani Abun A-zo-a-gani Na Tallafawa Farfadowar Nahiyar Afirka

Related

Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

5 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Sin Na Fatan Amurka Na Yin Wani Abun A-zo-a-gani Na Tallafawa Farfadowar Nahiyar Afirka

Sin Na Fatan Amurka Na Yin Wani Abun A-zo-a-gani Na Tallafawa Farfadowar Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.