• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadatar Abinci: Mun Zuba Naira Biliyan 309 Cikin Shekara 1 A Fannin Noma – Ministan Gona

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya bayyana cewa, a shekarar da ta gabata, Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu, ta zuba zunzurutun kudi kiminin Naira biliyan 309 a fannin aikin noma; domin samar da wadataccen abinci a Nijeriya.

Kyari, ya sanar da hakan ne; a matsayin guda daga cikin nasarorin da ma’aikatarsa ta samu a cikin shekara daya, wanda har ila yau kuma yake nuna nasarar da Shugaba Tinubu ya samu a zangonsa na shekara daya.

  • Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwalejin Noma Da Duba Aikin Babban Asibitin Maradun
  • Sanata Saliu Ya Raba Taki Da Injinan Ban Ruwa Ga Manoman Kwara

Ya ce, kokarin da ake yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki, gwamnatin tarayya ta kaddamar da aikin noman rani; wanda aka noma Alkama a kadada 118,657 da suke a jihohin wannan kasa sha biyar, musamman don noman da zai dauki har tsawon zagayowar wata shekarar.

Ministan ya kara da cewa, gwamnatin ta kuma rabar da tan 58,500 na Shinkafa a daukacin jihohin wannan kasa, ciki har da Abuja da nufin karya farashinta tare kuma da rabar da sauran kayayyakin abinci masu dauke da sinadarin ‘Bitamin A’.

Kyari ya ci gaba da cewa, a kokkarin dakile hauhawar farashin kayan abinci, gwamnatin ta kuma rabar da tan 60,432 na ingantaccen Irin noma kimanin tan 887,255.
”Gwamnatin ta kuma rabar da buhunhunan takin gargajiya kimanin 62,328, da kuma kayan aikin noma ga manoma a wannan fannin na noma, domin samun riba tare da kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

“Domin a samar da ingantaccen tsaro a gonakin manoma, an kara wa jami’an ‘yan sa kai da ke bayar da tsaro a wadannan gonaki na manoma, wato wadanda ake kira a turance ‘agro rangers’ da kuma sauran jami’an tsaron da ke aikin bayar da tsaro a gonakin kudade”, a cewar Kyari.

Kazalika Ministan ya bayyana cewa, gwamnati ta yi matukar kokari wajen bunkasa fannin kiwo da kula da lafiyar dabbobi tare kuma da kara karfafa gudanar da yin bincike a fannin kiwo da sauran ayyukan da suka shafi fannin kiwon.

Haka zalika a cewar tasa, gwamnati ta kara kaimi kwarai da gaske a wannan fanni na noma tare kuma da sarrafa Waken Soya, Kantu, Citta, Zobo da sauran kayayyakin amfanin gona, don a rika fitar da su kasashen waje ana sayarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zimbabwe Ta Yaba Da Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Bangaren Makamashi Mai Tsafta Na Kasar

Next Post

Sin Na Fatan Amurka Na Yin Wani Abun A-zo-a-gani Na Tallafawa Farfadowar Nahiyar Afirka

Related

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

1 week ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 week ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

2 weeks ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Next Post
Sin Na Fatan Amurka Na Yin Wani Abun A-zo-a-gani Na Tallafawa Farfadowar Nahiyar Afirka

Sin Na Fatan Amurka Na Yin Wani Abun A-zo-a-gani Na Tallafawa Farfadowar Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

July 1, 2025
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.