ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadatar Abinci: Mun Zuba Naira Biliyan 309 Cikin Shekara 1 A Fannin Noma – Ministan Gona

by Abubakar Abba
2 years ago
Abinci

Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya bayyana cewa, a shekarar da ta gabata, Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu, ta zuba zunzurutun kudi kiminin Naira biliyan 309 a fannin aikin noma; domin samar da wadataccen abinci a Nijeriya.

Kyari, ya sanar da hakan ne; a matsayin guda daga cikin nasarorin da ma’aikatarsa ta samu a cikin shekara daya, wanda har ila yau kuma yake nuna nasarar da Shugaba Tinubu ya samu a zangonsa na shekara daya.

  • Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwalejin Noma Da Duba Aikin Babban Asibitin Maradun
  • Sanata Saliu Ya Raba Taki Da Injinan Ban Ruwa Ga Manoman Kwara

Ya ce, kokarin da ake yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki, gwamnatin tarayya ta kaddamar da aikin noman rani; wanda aka noma Alkama a kadada 118,657 da suke a jihohin wannan kasa sha biyar, musamman don noman da zai dauki har tsawon zagayowar wata shekarar.

ADVERTISEMENT

Ministan ya kara da cewa, gwamnatin ta kuma rabar da tan 58,500 na Shinkafa a daukacin jihohin wannan kasa, ciki har da Abuja da nufin karya farashinta tare kuma da rabar da sauran kayayyakin abinci masu dauke da sinadarin ‘Bitamin A’.

Kyari ya ci gaba da cewa, a kokkarin dakile hauhawar farashin kayan abinci, gwamnatin ta kuma rabar da tan 60,432 na ingantaccen Irin noma kimanin tan 887,255.
”Gwamnatin ta kuma rabar da buhunhunan takin gargajiya kimanin 62,328, da kuma kayan aikin noma ga manoma a wannan fannin na noma, domin samun riba tare da kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa baki-daya.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

“Domin a samar da ingantaccen tsaro a gonakin manoma, an kara wa jami’an ‘yan sa kai da ke bayar da tsaro a wadannan gonaki na manoma, wato wadanda ake kira a turance ‘agro rangers’ da kuma sauran jami’an tsaron da ke aikin bayar da tsaro a gonakin kudade”, a cewar Kyari.

Kazalika Ministan ya bayyana cewa, gwamnati ta yi matukar kokari wajen bunkasa fannin kiwo da kula da lafiyar dabbobi tare kuma da kara karfafa gudanar da yin bincike a fannin kiwo da sauran ayyukan da suka shafi fannin kiwon.

Haka zalika a cewar tasa, gwamnati ta kara kaimi kwarai da gaske a wannan fanni na noma tare kuma da sarrafa Waken Soya, Kantu, Citta, Zobo da sauran kayayyakin amfanin gona, don a rika fitar da su kasashen waje ana sayarwa.

Abinci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Sin Na Fatan Amurka Na Yin Wani Abun A-zo-a-gani Na Tallafawa Farfadowar Nahiyar Afirka

Sin Na Fatan Amurka Na Yin Wani Abun A-zo-a-gani Na Tallafawa Farfadowar Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.