ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwalejin Noma Da Duba Aikin Babban Asibitin Maradun

by Leadership Hausa
2 years ago
gwamna

A ci gaba da bukukuwan cika shekara ɗaya a karagar mulkin jihar Zamfara, Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da manyan ayyuka biyu a Ƙananan Hukumomin Bakura da Maradun da ke yankin Zamfara ta Yamma.

Manyan ayyukan na cikin waɗanda Gwamnatin Dauda Lawal ta aiwatar cikin shekara guda.

A wata sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa gwamnan ya ziyarci ƙananan hukumomi uku: Mafara, Bakura, da Maradun.

ADVERTISEMENT

A Ƙaramar Hukumar Talatan Mafara, Gwamna Lawal ya nuna matuƙar damuwarsa kan yadda ya sami babban asibitin ƙaramar hukumar a lalace.

“A yau, a ci gaba da ƙaddamar da wasu ayyuka da aka kammala a shekarar farko da Gwamna Lawal ya yi kan mulki, Gwamnan tare da rakiyar tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Ahmad Sani Yariman Bakura, sun ƙaddamar da sabuwar Kwalejin Noma da Fasaha da aka gyara a garin Bakura.”

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara

A jawabinsa wajen ƙaddamar da kwalejin, Gwamna Lawal ya ce; sama da shekaru ashirin da kafa Kwalejin Noma ta Bakura, tsarinta ya lalace, inda ba za a iya koyo ko koyarwa a muhallin ba.

gwamna

“A matsayinmu na gwamnatin da ta bayyana ilimi da noma a cikin manyan abubuwan da ta sa a gaba, mun ga ya dace a gyara kwalejin tare da adana mata muhimman abubuwan da za a samar da ingantaccen ilimin aikin gona.

“Mun kuma ɗaga darajar Cibiyar daga Kwalejin Noma da Kimiyyar Dabbobi zuwa Kwalejin Noma da Fasaha ta Bakura. Hikimar da ke tattare da wannan ita ce bai wa kwalejin damar gabatar da wasu fasahohi a matsayin abin da ake buƙata don sauye-sauyen ɗaga fasahar zamani a kwalejin.

“Saboda haka, a yau mun taru a nan domin ƙaddamar da ayyukan gyare-gyaren da aka gudanar a kwalejin. Waɗannan sun haɗa da gyara ɓangaren masu gudanarwa, ɗakin gwaje-gwajen iri da sauran abubuwan da suka shafi noma, ɗakin gwaje-gwajen ƙwayoyin halitta, ɗakin gwaje-gwajen abubuwan da suka shafi kimiyya, babban ɗakin lakca da ɗakunan kwanan ɗalibai. Har ila yau, an gina wasu bankunan manyan baƙi guda biyar tare da inganta tsarin ruwa na kwalejin.”

Yayin da yake a ƙaramar hukumar Maradun, Gwamna Lawal ya yi dubi da yadda ake gudanar da aikin gyaran babban asibitin Maradun.

gwamna

“Kwangilar aikin ta haɗa da gyaran ɓangaren masu gudanarwa, ɗakunan majiyyata maza da mata, ɗakunan kwana na ma’aikata, ɗakin ajiyar gawa, babban ɗakin tiyata, da banɗakuna guda biyu. Sauran ayyukan sun haɗa da katange asibitin, samar da isasshen ruwa na asibitin, hanyoyin tafiya da kayan aiki gaba ɗaya.”

A ƙaramar hukumar Talatan Mafara, gwamna Lawal ya nuna rashin gamsuwa da rashin jin daɗin sa a kan halin da babban asibitin Talatan Mafara yake, inda nan take ya bada umarnin gyara da inganta shi.

“Akwai matuƙar tada hankali ganin halin da babban asibitin Talatan Mafara ke ciki. Ba zan lamunci irin halin da na ga asibiti a ciki ba a lokacin bincike na. Abin da ke nuni da yadda ’yan siyasarmu ke karkatar da dukiyar ƙasa, waɗanda galibi suke aiwatar da al’amura marasa muhimmanci.

“Na ba da umarnin gyara da inganta asibitin nan take. Za mu samar da kayan aikin asibitin don samar da gyara da kuma zama babban jigo ga sauran cibiyoyin kiwon lafiya a yammacin jihar. Inganta yanayin sa zai samar da tsayayyen kiwon lafiya a yankin.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
NLC Ta Bukaci A Kara Wa ‘Yan Jarida Albashi, Inshora Da Fansho

NLC Ta Bukaci A Kara Wa 'Yan Jarida Albashi, Inshora Da Fansho

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.