• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye Game Da Yadda Kasar Sin Ta Tallafawa Duniya A Fanin Yaki Da Annobar COVID-19

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan barkewar annobar COVID-19, kasashen duniya sun dukafa wajen ganin bayan cutar, ta hanyar daukar matakai daban daban a lokuta mabanbanta, kuma matakin samar da alluran rigakafi masu inganci na sahun gaba a wannan muhimmin aiki.

Cikin kusan shekaru uku da suka gabata, kasar Sin ta yi rawar gani a fannin bincike da samar da rigakafin COVID-19, inda ta sauke nauyin dake wuyanta ta fuskar samar da rigakafi mai inganci ga alummun duniya baki daya.

  • Me Ya Sa Kasar Sin Ta Dinga Yaki Da Cutar COVID-19 Har Tsawon Shekaru Uku?

Cikin shekarar 2020, masu binciken kimiyya na kasar Sin sun kirkiro tare da gwada nauoin rigakafin wannan annoba daban daban, inda ya zuwa watan Mayun shekarar 2021 da ta gabata, hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, ta sanya rigakafin Sinopharm cikin jerin rigakafin COVID-19 da aka amince a yi amfani da su a mataki na gaggawa. Rigakafin da ya zama na farko samfurin kasar Sin da WHO ta amince da shi, kuma na 6 a duniya da ya samu amincewar hukumar.

Daga bisani, kamfanin Sinovac ya sake fitar da karin rigakafin cutar ta COVID-19, wanda shi ma ya samu amincewar hukumar WHO domin amfani da shi a matakin gaggawa.

Idan an kwatanta da wasu nauo’in rigakafin cutar COVID-19 na kamfanonin Moderna da Pfizer, samfurin rigakafin kasar Sin na da fifito, kasancewar za a iya daukar sa daga wuri zuwa wuri cikin naurorin sanyaya abubuwa na amfanin yau da kullum, ba tare da sun lalace ba. Hakan na nufin rigakafin na Sin sun dace da yanayi irin na kasashe masu tasowa, wadanda ke da karancin wuraren adana rigakafi dake da bukatar wuraren ajiya masu sanyin gaske.

Labarai Masu Nasaba

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

A daya bangaren kuma, tun bayan da kasar Sin ta shiga shirin samar da daidaito wajen rarraba rigakafin annobar COVID-19 wato shirin COVAX” a watan Oktoban shekarar 2020, kasar ta ci gaba da mika kyautar rigakafin cutar ga sassa daban daban na duniya. A watan Agustan shekarar bara, Sin ta alkawarta ba da tallafin rigakafin COVID-19, wanda darajarsa ta kai dalar Amurka biliyan biyu ga kasashen duniya daban daban, tare da karin tallafin dala miliyan 100 ga shirin na COVAX.

Ya zuwa watan Mayun shekarar 2022, Sin ta samar da tallafin kayayyakin yaki da annobar ga kasashe 153, da hukumomin kasa da kasa masu nasaba da wannan aiki har 15.

Kasar Sin ta bayar da agajin rigakafin COVID-19 guda biliyan 2.2 ga kasashe daban daban. Kaza lika ta tura tawagogin kiwon lafiya zuwa kasashe 34, ta kuma rarraba kwarewar wannan muhimmin aiki na yakin da cutar tare da kasashen duniya sama da 180, da ma wasu hukumomin kasa da kasa, matakan da dukkaninsu suka yi matukar samun yabo daga daukacin sassan duniya, musamman ma kasashe masu tasowa wadanda su ne suka fi cin gajiya daga wadannan tallafi na Sin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Kasar Sin Ta Dinga Yaki Da Cutar COVID-19 Har Tsawon Shekaru Uku?

Next Post

Shugabannin Nijeriya Da Nijar Za Su Bude Gasar Karatun Kur’ani A Zamfara Gobe Juma’a

Related

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

60 minutes ago
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

2 hours ago
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya
Daga Birnin Sin

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

4 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

4 hours ago
Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci
Daga Birnin Sin

Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

6 hours ago
An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

22 hours ago
Next Post
Shugabannin Nijeriya Da Nijar Za Su Bude Gasar Karatun Kur’ani A Zamfara Gobe Juma’a

Shugabannin Nijeriya Da Nijar Za Su Bude Gasar Karatun Kur'ani A Zamfara Gobe Juma'a

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

May 28, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

May 28, 2025
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

May 28, 2025
An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda

An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda

May 28, 2025
Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

May 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.