ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye Game Da Yadda Kasar Sin Ta Tallafawa Duniya A Fanin Yaki Da Annobar COVID-19

by CMG Hausa
4 years ago

Tun bayan barkewar annobar COVID-19, kasashen duniya sun dukafa wajen ganin bayan cutar, ta hanyar daukar matakai daban daban a lokuta mabanbanta, kuma matakin samar da alluran rigakafi masu inganci na sahun gaba a wannan muhimmin aiki.

Cikin kusan shekaru uku da suka gabata, kasar Sin ta yi rawar gani a fannin bincike da samar da rigakafin COVID-19, inda ta sauke nauyin dake wuyanta ta fuskar samar da rigakafi mai inganci ga alummun duniya baki daya.

  • Me Ya Sa Kasar Sin Ta Dinga Yaki Da Cutar COVID-19 Har Tsawon Shekaru Uku?

Cikin shekarar 2020, masu binciken kimiyya na kasar Sin sun kirkiro tare da gwada nauoin rigakafin wannan annoba daban daban, inda ya zuwa watan Mayun shekarar 2021 da ta gabata, hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, ta sanya rigakafin Sinopharm cikin jerin rigakafin COVID-19 da aka amince a yi amfani da su a mataki na gaggawa. Rigakafin da ya zama na farko samfurin kasar Sin da WHO ta amince da shi, kuma na 6 a duniya da ya samu amincewar hukumar.

ADVERTISEMENT

Daga bisani, kamfanin Sinovac ya sake fitar da karin rigakafin cutar ta COVID-19, wanda shi ma ya samu amincewar hukumar WHO domin amfani da shi a matakin gaggawa.

Idan an kwatanta da wasu nauo’in rigakafin cutar COVID-19 na kamfanonin Moderna da Pfizer, samfurin rigakafin kasar Sin na da fifito, kasancewar za a iya daukar sa daga wuri zuwa wuri cikin naurorin sanyaya abubuwa na amfanin yau da kullum, ba tare da sun lalace ba. Hakan na nufin rigakafin na Sin sun dace da yanayi irin na kasashe masu tasowa, wadanda ke da karancin wuraren adana rigakafi dake da bukatar wuraren ajiya masu sanyin gaske.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

A daya bangaren kuma, tun bayan da kasar Sin ta shiga shirin samar da daidaito wajen rarraba rigakafin annobar COVID-19 wato shirin COVAX” a watan Oktoban shekarar 2020, kasar ta ci gaba da mika kyautar rigakafin cutar ga sassa daban daban na duniya. A watan Agustan shekarar bara, Sin ta alkawarta ba da tallafin rigakafin COVID-19, wanda darajarsa ta kai dalar Amurka biliyan biyu ga kasashen duniya daban daban, tare da karin tallafin dala miliyan 100 ga shirin na COVAX.

Ya zuwa watan Mayun shekarar 2022, Sin ta samar da tallafin kayayyakin yaki da annobar ga kasashe 153, da hukumomin kasa da kasa masu nasaba da wannan aiki har 15.

Kasar Sin ta bayar da agajin rigakafin COVID-19 guda biliyan 2.2 ga kasashe daban daban. Kaza lika ta tura tawagogin kiwon lafiya zuwa kasashe 34, ta kuma rarraba kwarewar wannan muhimmin aiki na yakin da cutar tare da kasashen duniya sama da 180, da ma wasu hukumomin kasa da kasa, matakan da dukkaninsu suka yi matukar samun yabo daga daukacin sassan duniya, musamman ma kasashe masu tasowa wadanda su ne suka fi cin gajiya daga wadannan tallafi na Sin.

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Shugabannin Nijeriya Da Nijar Za Su Bude Gasar Karatun Kur’ani A Zamfara Gobe Juma’a

Shugabannin Nijeriya Da Nijar Za Su Bude Gasar Karatun Kur'ani A Zamfara Gobe Juma'a

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.