ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye Game Da Yadda Kasar Sin Ta Tallafawa Duniya A Fanin Yaki Da Annobar COVID-19

by CMG Hausa
4 years ago

Tun bayan barkewar annobar COVID-19, kasashen duniya sun dukafa wajen ganin bayan cutar, ta hanyar daukar matakai daban daban a lokuta mabanbanta, kuma matakin samar da alluran rigakafi masu inganci na sahun gaba a wannan muhimmin aiki.

Cikin kusan shekaru uku da suka gabata, kasar Sin ta yi rawar gani a fannin bincike da samar da rigakafin COVID-19, inda ta sauke nauyin dake wuyanta ta fuskar samar da rigakafi mai inganci ga alummun duniya baki daya.

  • Me Ya Sa Kasar Sin Ta Dinga Yaki Da Cutar COVID-19 Har Tsawon Shekaru Uku?

Cikin shekarar 2020, masu binciken kimiyya na kasar Sin sun kirkiro tare da gwada nauoin rigakafin wannan annoba daban daban, inda ya zuwa watan Mayun shekarar 2021 da ta gabata, hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, ta sanya rigakafin Sinopharm cikin jerin rigakafin COVID-19 da aka amince a yi amfani da su a mataki na gaggawa. Rigakafin da ya zama na farko samfurin kasar Sin da WHO ta amince da shi, kuma na 6 a duniya da ya samu amincewar hukumar.

ADVERTISEMENT

Daga bisani, kamfanin Sinovac ya sake fitar da karin rigakafin cutar ta COVID-19, wanda shi ma ya samu amincewar hukumar WHO domin amfani da shi a matakin gaggawa.

Idan an kwatanta da wasu nauo’in rigakafin cutar COVID-19 na kamfanonin Moderna da Pfizer, samfurin rigakafin kasar Sin na da fifito, kasancewar za a iya daukar sa daga wuri zuwa wuri cikin naurorin sanyaya abubuwa na amfanin yau da kullum, ba tare da sun lalace ba. Hakan na nufin rigakafin na Sin sun dace da yanayi irin na kasashe masu tasowa, wadanda ke da karancin wuraren adana rigakafi dake da bukatar wuraren ajiya masu sanyin gaske.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

A daya bangaren kuma, tun bayan da kasar Sin ta shiga shirin samar da daidaito wajen rarraba rigakafin annobar COVID-19 wato shirin COVAX” a watan Oktoban shekarar 2020, kasar ta ci gaba da mika kyautar rigakafin cutar ga sassa daban daban na duniya. A watan Agustan shekarar bara, Sin ta alkawarta ba da tallafin rigakafin COVID-19, wanda darajarsa ta kai dalar Amurka biliyan biyu ga kasashen duniya daban daban, tare da karin tallafin dala miliyan 100 ga shirin na COVAX.

Ya zuwa watan Mayun shekarar 2022, Sin ta samar da tallafin kayayyakin yaki da annobar ga kasashe 153, da hukumomin kasa da kasa masu nasaba da wannan aiki har 15.

Kasar Sin ta bayar da agajin rigakafin COVID-19 guda biliyan 2.2 ga kasashe daban daban. Kaza lika ta tura tawagogin kiwon lafiya zuwa kasashe 34, ta kuma rarraba kwarewar wannan muhimmin aiki na yakin da cutar tare da kasashen duniya sama da 180, da ma wasu hukumomin kasa da kasa, matakan da dukkaninsu suka yi matukar samun yabo daga daukacin sassan duniya, musamman ma kasashe masu tasowa wadanda su ne suka fi cin gajiya daga wadannan tallafi na Sin.

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
Shugabannin Nijeriya Da Nijar Za Su Bude Gasar Karatun Kur’ani A Zamfara Gobe Juma’a

Shugabannin Nijeriya Da Nijar Za Su Bude Gasar Karatun Kur'ani A Zamfara Gobe Juma'a

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.