• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye Kan Gudummawar Kasar Sin Game Da Ingiza Hadin Gwiwa Don Bunkasa Shawarar Raya Ci Gaban Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Waiwaye Kan Gudummawar Kasar Sin Game Da Ingiza Hadin Gwiwa Don Bunkasa Shawarar Raya Ci Gaban Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Samar da ci gaban rayuwa buri ne na daukacin bil adama. Kaza lika, daya ne daga muhimman ginshikai da daukacin kasashen duniya ke fatan cimmawa, kuma manufa ce da ba a kawo karshenta a tsawon tarihin rayuwar dan Adam a doron kasa.

 

Tun bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar nan ta raya ci gaban duniya wato “Global Development Initiative” ko GDI a takaice, yayin zaman muhawara na babban taron MDD karo na 76 a watan Satumban shekarar 2021, Sin ta ci gaba da samar da gudummawa bisa basirarta da karfinta na tunkarar batutuwan ci gaban kasa da kasa. A bana shekaru 3 ke nan bayan gabatar da wannan shawara ta GDI, kuma har yanzu ana ta kokarin karfafa matakan cimma nasararta.

  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Mai Nazarin Duniyar Dan Adam
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Kwamitin Kasa Na Shirya Liyafar Karrama Gwaraza A Fannin Raya Alakar Sin Da Amurka

Baya ga kasar Sin da ta gabatar da shawarar GDI, sassan kasa da kasa na ci gaba da rungumar shawarar, kawo yanzu kasashe da hukumomin kasa da kasa da suka nuna goyon bayansu ga wannan shawara sun haura 100, suna kuma ci gaba da karuwa, baya ga kasashe sama da 80 da suka shiga kawancen tabbatar da nasarar wannan shawara.

 

Labarai Masu Nasaba

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Masharhanta na jinjinawa kwazon kasar Sin bisa aiki da take yi tukuru tare da sauran abokan tafiya, musamman ganin yadda karkashin wannan shawara ta GDI, Sin ke ta fadada zuba jari ga ayyukan da suka shafi shawarar, inda adadin ayyukan bunkasa ci gaban duniya masu nasaba da ita suka zarce 1,000. Baya ga hakan, mun ga yadda Sin ta aiwatar da wasu ayyuka na hadin gwiwa tsakanin sassa 3, wato Sin da daidaikun kasashe, da kuma wasu hukumomin kasa da kasa da yawansu ya haura 140, ayyukan da aka gudanar da su a sama da kasashe 60.

 

Baya ga haka, kasar Sin ta samar da cibiyoyin horas da fasahohin kere-kere masu dacewa da aikin ingiza shawarar ta GDI, don baiwa dimbin al’ummun duniya damar cin gajiyar shawarar a kasashe masu tasowa. Bisa wannan shiri, an bude cibiyoyin koyar da sanin makaman aiki sama da 1,000 a irin wadannan kasashe, inda tuni kwararru sama da 40,000 suka ci gajiyar horo daga wadannan cibiyoyi.

 

Yayin da shawarar GDI ke samun tagomashi tsakanin sassan kasa da kasa, kuma take kara zurfafa hadin gwiwa da dukkanin sassa wajen yayata cin gajiya daga gare ta, ko shakka babu duniya za ta ci gaba da more damammakin zamanintarwa irin na kasar Sin, a daya hannu Sin da sauran sassan duniya za su ci gaba da dunkule wajen raba gajiyarsu.

 

Fatan dukkanin sassan kasa da kasa dai shi ne shawarar GDI, da makamantanta za su ci gaba da cimma nasara, su kuma dunkule tare da manyan manufofin bunkasa duniya, irinsu ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan zuwa shekarar 2030, da ajandar bunkasa kasashen Afirka ta kungiyar AU ta nan da shekarar 2063 da sauransu, ta yadda kasar Sin da sauran sassan kasa da kasa, za su kai ga kara ingiza ci gaban duniya bisa daidaito, da adalci, har a kai ga gina duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin

Next Post

A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Related

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

19 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

20 hours ago
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

20 hours ago
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

21 hours ago
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

22 hours ago
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

23 hours ago
Next Post
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.