• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin: Kuri’ar Kin Amincewar Da Amurka Ta Jefa Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza Ta Rushe Matsayar Kwamitin Sulhun MDD

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakilin Sin: Kuri’ar Kin Amincewar Da Amurka Ta Jefa Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza Ta Rushe Matsayar Kwamitin Sulhun MDD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin sulhu na MDD ya kada kuri’a game da daftarin kudurin tsagaita wuta a Gaza nan da nan, wanda kasar Aljeriya ta gabatar a madadin kasashen Larabawa, to sai kuma ba a zartas da kudurin ba sakamakon kuri’ar kin amincewar da Amurka ta jefa.

Zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Zhang Jun, ya jefa kuri’ar amincewa da kudurin, kana ya ba da jawabi don bayyana matsayin bangaren Sin. Zhang Jun ya ce bangaren Sin ya yi bakin ciki sosai game da yadda Amurka ta ki amincewa da daftarin.

  • Cibyar Dakon Kaya Da Kasar Sin Ta Gina Na Taimakawa Bunkasar Kayayyakin Da Ake Fitarwa A Kasar Uganda
  • Don Tabbatar Da Adalci A Duniya Ana Bukatar Hadin Gwiwar “Global South”

Daftarin kudurin da Aljeriya ta gabatar a madadin kasashen Larabawa, na bukatar tsagaita wuta a Gaza nan da nan, da saki dukkan mutanen da ake tsare da su, da shigar da kayayyakin jin kai, da kuma hana tilastawa jama’a canja matsuguni, wannan ba ma kawai bukata ce ta gaggawa game da yanayin da ake ciki a yanzu ba ne, har ma yana da alaka da samar da abubuwan bukatun jin kai, don haka ya kamata dukkan mambobin kwamitin sulhun su nuna goyon baya ga kudurin.

Sakamakon jefa kuri’un ya nuna cewa, kwamitin sulhun MDD ya cimma matsaya guda daya kan batun, amma Amurka ta rushe matsayar. Ya ce matakin na Amurka ya jefa Gaza cikin yanayi mai hadari.

A yayin jefa kuri’ar ta wannan karo, daftarin kudurin da Aljeriya ta gabatar ya samu kuri’un amincewa 13, ciki har da kuri’ar kasar Sin, yayin da Birtaniya ta janye jiki daga jefa kuri’a.

Labarai Masu Nasaba

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Game da batun, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a taron manema labaru yau Laraba cewa, Amurka ta sake yin fatali da daftarin kudurin kwamitin sulhu na MDD kan zirin Gaza, lamarin da ya sa al’ummar Gaza cikin wani yanayi mai hadari.

Da take karin haske kan wannan tambaya, Mao Ning ta yi nuni da cewa, halin da ake ciki na jin kai a Gaza, yana da matukar muni, kuma zaman lafiya da kwanciyar hankali na yankin ya yi tasiri sosai. Tilas ne kwamitin sulhun ya dauki matakai cikin gaggawa don inganta tsagaita bude wuta da kuma kawo karshen yakin.

Mao ta ce, kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa da dukkan bangarori na kasa da kasa, wajen ingiza kwamitin sulhu na MDD ya dauki matakan da suka dace, da yin kokarin kawo karshen yakin Gaza nan da nan, da sassauta yanayin jin kai, da sa kaimi ga aiwatar da shirin kafa kasashe biyu da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali na dogon lokaci a yankin Gabas ta Tsakiya. (Ibrahim Yaya, Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GazaIsra'ilawaMDDNATO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabuwar Shugabar Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙasa.

Next Post

Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

Related

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
Daga Birnin Sin

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

4 hours ago
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

5 hours ago
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
Daga Birnin Sin

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

7 hours ago
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

9 hours ago
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

17 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

17 hours ago
Next Post
Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

Mun Hana Kai Wa 'Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba - Dauda

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.