ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

by Leadership Hausa
2 years ago
Dauda

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bayyana cewa babu inda gwamnatin sa ta hana yi ko sayar da biredi a duk faɗin jihar.

Wannan ya biyo bayan wata sanarwa ce da ƙungiyar masu gidajen biredi ta jihar Zamfara ta fitar, inda suka shelanta dakatar da gasa biredin sakamakon haramta tallar sa da gwamnatin ta yi a bisa babura, wanda kuma gwamnatin ta ce ta yi haka ne don ta katse hanyoyin da ake kai wa ‘yan ta’adda biredin.

  • Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar
  • Gwamnatin Zamfara Za Ta Yi Haɗin Gwiwa Da Ƙasar Sweden Kan Haƙar Ma’adanai Da Noma

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya bayyana cewa gwamnatin ba ta ɗauki wannan matakin da wata mummunar manufa b ne, illa don ta toshe hanyoyin da ake kai wa ‘yan ta’adda kayan masarufi a duk faɗin jihar.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta Idris ta ƙara da cewa gwamnatin ta haramta sayar da biredi da man fetur a wuraren da ta’addancin ya yi ƙamari ne don a toshe hanyoyin da ‘yan ta’addan ke samun kayan masarufi.

Sanarwar ta ƙara sa cewa, “Gwamnatin jijar Zamfara na so ta yi ƙarin haske game da surutan sa ke yawo, inda ake zargin cewa gwamnatin ta hana masu gidaje biredi yi a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

“Gwamnatin na ƙalubalantar waɗannan labarai da cewa ba gaskiya ba ne, wanda ke kuma jawo ruɗani a tsakanin jama’a da su kan su masu gidajen biredin.

“Gwamnatin jihar Zamfara ba ta da wata niyya ta tsoma baki a harkar gasawa ko sayar da biredi, wanda biredi a yanzu ya zama shi ne kusan abincin kowane gida.

“Bugu da ƙari, mu na so mu tabbatar wa al’umma cewa kullum ƙoƙarin gwamnati, shi ne fito da hanyoyin da za ta inganta harkokin kasuwanci da hanyoyin cin abinci ga al’ummar ta. Mu na sane da irin gudumawar da ƙananan masana’antu ke bayarwa ga ci gaban tattalin arziki, kuma mun jajirce wajen ganin mun ƙarfafa masu gwiwa don cimma nasarar su.

“Kuma duk da haka, mun fito da wasu hanyoyi da dama na yaƙar ‘yan ta’adda masu kawo mana ruɗani a wasu sassan jihar nan.

“Waɗannan hanyoyi kuwa, sun haɗa da haramta sayar da biredi da man fetur a wasu wurare da ba a natsu da su ba, ba domin komai ba, sai don a takura wa waɗannan shaiɗanu, domin sun dogara ne da waɗannan muhimman abubuwa wajen aiwatar da Ta’addancin su.

“Gwamnatin jihar Zamfara na da fatan cewa sakamakon aiwatar da wannan haramci, za ta iya dawo da zaman lafiya a waɗannan wurare, don kare rayuka da dukiyar jama’a. Wannan haramci da aka ambata, yana daga dabarun da ake sa ran cimma nasarar wannan yaƙi.”

Dauda
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.