ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

by Leadership Hausa
2 years ago
Dauda

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bayyana cewa babu inda gwamnatin sa ta hana yi ko sayar da biredi a duk faɗin jihar.

Wannan ya biyo bayan wata sanarwa ce da ƙungiyar masu gidajen biredi ta jihar Zamfara ta fitar, inda suka shelanta dakatar da gasa biredin sakamakon haramta tallar sa da gwamnatin ta yi a bisa babura, wanda kuma gwamnatin ta ce ta yi haka ne don ta katse hanyoyin da ake kai wa ‘yan ta’adda biredin.

  • Hukumar Hisbah A Zamfara Ta Hana ‘Ƙauye Day’ Da Sauran Bukukuwan Aure Da Ba Su Cancanta Ba A Jihar
  • Gwamnatin Zamfara Za Ta Yi Haɗin Gwiwa Da Ƙasar Sweden Kan Haƙar Ma’adanai Da Noma

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya bayyana cewa gwamnatin ba ta ɗauki wannan matakin da wata mummunar manufa b ne, illa don ta toshe hanyoyin da ake kai wa ‘yan ta’adda kayan masarufi a duk faɗin jihar.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta Idris ta ƙara da cewa gwamnatin ta haramta sayar da biredi da man fetur a wuraren da ta’addancin ya yi ƙamari ne don a toshe hanyoyin da ‘yan ta’addan ke samun kayan masarufi.

Sanarwar ta ƙara sa cewa, “Gwamnatin jijar Zamfara na so ta yi ƙarin haske game da surutan sa ke yawo, inda ake zargin cewa gwamnatin ta hana masu gidaje biredi yi a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

“Gwamnatin na ƙalubalantar waɗannan labarai da cewa ba gaskiya ba ne, wanda ke kuma jawo ruɗani a tsakanin jama’a da su kan su masu gidajen biredin.

“Gwamnatin jihar Zamfara ba ta da wata niyya ta tsoma baki a harkar gasawa ko sayar da biredi, wanda biredi a yanzu ya zama shi ne kusan abincin kowane gida.

“Bugu da ƙari, mu na so mu tabbatar wa al’umma cewa kullum ƙoƙarin gwamnati, shi ne fito da hanyoyin da za ta inganta harkokin kasuwanci da hanyoyin cin abinci ga al’ummar ta. Mu na sane da irin gudumawar da ƙananan masana’antu ke bayarwa ga ci gaban tattalin arziki, kuma mun jajirce wajen ganin mun ƙarfafa masu gwiwa don cimma nasarar su.

“Kuma duk da haka, mun fito da wasu hanyoyi da dama na yaƙar ‘yan ta’adda masu kawo mana ruɗani a wasu sassan jihar nan.

“Waɗannan hanyoyi kuwa, sun haɗa da haramta sayar da biredi da man fetur a wasu wurare da ba a natsu da su ba, ba domin komai ba, sai don a takura wa waɗannan shaiɗanu, domin sun dogara ne da waɗannan muhimman abubuwa wajen aiwatar da Ta’addancin su.

“Gwamnatin jihar Zamfara na da fatan cewa sakamakon aiwatar da wannan haramci, za ta iya dawo da zaman lafiya a waɗannan wurare, don kare rayuka da dukiyar jama’a. Wannan haramci da aka ambata, yana daga dabarun da ake sa ran cimma nasarar wannan yaƙi.”

Dauda
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

Shugaban Faransa Ya Gana Da Wang Yi

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.