Wakilin kasar Sin ya nuna rashin gamsuwa da abun da Amurka ta aikata wajen amincewa da kudurin kwamitin sulhun MDD game da takunkuman da aka kakaba wa Sudan ta Kudu a jiya Jumma’a.
Yayin da ake gudanar da tuntuba kan daftarin kudurin, wakilan kasashen Afirka na kwamitin sulhun sun ba da shawarar tsame takunkumin hana shigar da makamai da suka wajaba ga rundunonin sojan da suka dace, wanda mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya bayyana a matsayin mafita mai ma’ana kuma mai yiwuwa a halin da ake ciki.
Sai dai kuma, Amurka ta ki tattaunawa a kan ra’ayoyi masu ma’ana na kasashen yankin, yayin da ta kafe kai da fata a kan ci gaba da kakaba takunkuman.
Sun ya kara da cewa, wakilin kasar bai taba neman rubutattun sharhohin da aka yi a kan rubutun daftarin kudurin daga sauran mambobin kwamitin ba, amma ya matsa kaimi wajen ganin an kada kuri’a duk da cewa har yanzu akwai sabani a tsakanin mambobin, wanda hakan bai dace da tsarin gudanarwa na kwamitin sulhun ba. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp