• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Kashe Budurwa Ya Boye Gawarta A Tankin Ruwa Ya Shiga Hannu

by Abubakar Abba
3 years ago
Budurwa

‘Yansanda a Jihar Koros Ribas sun kama wani dan shekara 49 mai suna Eyo Etim, bisa zarginsa da kashe wata budurwa mai suna Harmony Edemawan a yankin Atim da ke karamar hukumar Akpabuyo.

An ruwaito cewa, wanda ake zargin an cafke shi ne a ranar bikin Kirisimeti.

  • Liverpool Ta Sayi Cody Gakpo Daga PSV
  • Masu Son Gwamnatin Tarayya Ta Yi Magudi A Zaben Bauchi, Ba Za Su Yi Nasara Ba – Bala Mohammed 

Wata majiya a karamar hukumar Akpabuyo, ta shaida wa LEADERSHIP cewa, asirinsa ya tonu ne lokacin da wasu ‘yan sintiri a yankin suka gudanar da bincike a gidansa bayan an samu labarin bacewar budurwar.

A lokacin bincike, ‘yan sintirin sun ga jini a kasa gidan inda suka gayyato ‘yansanda zuwa gidan, nan take ‘yansandan suka bayar da umarnin bude tankin ruwan, inda aka ga gawar budurwar a cikin tankin.

Budurwar dai, ta kasance ma’aikaciya ce a kamfanin Lafarge Holcim, inda kuma bayan gano gawarta, ‘yansandan suka kama Eyo Etim bisa zarginsa da kitsa kashe Edemawan saboda bashin da yake binta.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

An ruwaito cewa, budurwar ta bace ne tun a ranar 22 ga watan Disamba, 2022.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Sule Balarabe, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, Eyo na hannunsu a yanzu.

Ya ce, Eyo ya basu bayanan karya na cewa, budurwar ta sayar da wata kadararsa da kudinta ya kai kimanin Naira miliyan tara sannan kuma taki biyansa.

Sule, ya kara da cewa, Eyo ya yi hayar wasu mutane su sace ta don ya karbi kudinsa, amma aka kashe ta aka kuma boye gawarta a cikin tankin ruwan, inda ya ce, ana ci gaba da bincike don a kamo sauran mutanen da hada baki da su don hallaka budurwar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, ya ranci bashin budurwar har kimanin Naira miliyan 1.2 wacce kuma aka ce, yana yin soyayya da wata ‘yar uwarta mai suna Ruth Edem ‘yar shekara 22 kuma daliba a jami’ar UNICAL.

Wani dan uwan budurwar da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya ce, Eyo ya ranci kudin budurwar kimanin Naira miliyan 1.2 a farkon wannan shekarar don bunkasa kasuwancinsa na sayar da manja.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

LABARAI MASU NASABA

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.