• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Kashe Budurwa Ya Boye Gawarta A Tankin Ruwa Ya Shiga Hannu

by Abubakar Abba
3 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Wanda Ya Kashe Budurwa Ya Boye Gawarta A Tankin Ruwa Ya Shiga Hannu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yansanda a Jihar Koros Ribas sun kama wani dan shekara 49 mai suna Eyo Etim, bisa zarginsa da kashe wata budurwa mai suna Harmony Edemawan a yankin Atim da ke karamar hukumar Akpabuyo.

An ruwaito cewa, wanda ake zargin an cafke shi ne a ranar bikin Kirisimeti.

  • Liverpool Ta Sayi Cody Gakpo Daga PSV
  • Masu Son Gwamnatin Tarayya Ta Yi Magudi A Zaben Bauchi, Ba Za Su Yi Nasara Ba – Bala Mohammed 

Wata majiya a karamar hukumar Akpabuyo, ta shaida wa LEADERSHIP cewa, asirinsa ya tonu ne lokacin da wasu ‘yan sintiri a yankin suka gudanar da bincike a gidansa bayan an samu labarin bacewar budurwar.

A lokacin bincike, ‘yan sintirin sun ga jini a kasa gidan inda suka gayyato ‘yansanda zuwa gidan, nan take ‘yansandan suka bayar da umarnin bude tankin ruwan, inda aka ga gawar budurwar a cikin tankin.

Budurwar dai, ta kasance ma’aikaciya ce a kamfanin Lafarge Holcim, inda kuma bayan gano gawarta, ‘yansandan suka kama Eyo Etim bisa zarginsa da kitsa kashe Edemawan saboda bashin da yake binta.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

An ruwaito cewa, budurwar ta bace ne tun a ranar 22 ga watan Disamba, 2022.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Sule Balarabe, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, Eyo na hannunsu a yanzu.

Ya ce, Eyo ya basu bayanan karya na cewa, budurwar ta sayar da wata kadararsa da kudinta ya kai kimanin Naira miliyan tara sannan kuma taki biyansa.

Sule, ya kara da cewa, Eyo ya yi hayar wasu mutane su sace ta don ya karbi kudinsa, amma aka kashe ta aka kuma boye gawarta a cikin tankin ruwan, inda ya ce, ana ci gaba da bincike don a kamo sauran mutanen da hada baki da su don hallaka budurwar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, ya ranci bashin budurwar har kimanin Naira miliyan 1.2 wacce kuma aka ce, yana yin soyayya da wata ‘yar uwarta mai suna Ruth Edem ‘yar shekara 22 kuma daliba a jami’ar UNICAL.

Wani dan uwan budurwar da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya ce, Eyo ya ranci kudin budurwar kimanin Naira miliyan 1.2 a farkon wannan shekarar don bunkasa kasuwancinsa na sayar da manja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaBincikeBudurwaKisaTankin Ruwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Uwan Juna 3 Bayan Biyan Kudin Fansa A Taraba

Next Post

CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

Related

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

1 week ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

4 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

1 month ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Next Post
CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.