• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Kashe Budurwa Ya Boye Gawarta A Tankin Ruwa Ya Shiga Hannu

by Abubakar Abba
3 years ago
Budurwa

‘Yansanda a Jihar Koros Ribas sun kama wani dan shekara 49 mai suna Eyo Etim, bisa zarginsa da kashe wata budurwa mai suna Harmony Edemawan a yankin Atim da ke karamar hukumar Akpabuyo.

An ruwaito cewa, wanda ake zargin an cafke shi ne a ranar bikin Kirisimeti.

  • Liverpool Ta Sayi Cody Gakpo Daga PSV
  • Masu Son Gwamnatin Tarayya Ta Yi Magudi A Zaben Bauchi, Ba Za Su Yi Nasara Ba – Bala Mohammed 

Wata majiya a karamar hukumar Akpabuyo, ta shaida wa LEADERSHIP cewa, asirinsa ya tonu ne lokacin da wasu ‘yan sintiri a yankin suka gudanar da bincike a gidansa bayan an samu labarin bacewar budurwar.

A lokacin bincike, ‘yan sintirin sun ga jini a kasa gidan inda suka gayyato ‘yansanda zuwa gidan, nan take ‘yansandan suka bayar da umarnin bude tankin ruwan, inda aka ga gawar budurwar a cikin tankin.

Budurwar dai, ta kasance ma’aikaciya ce a kamfanin Lafarge Holcim, inda kuma bayan gano gawarta, ‘yansandan suka kama Eyo Etim bisa zarginsa da kitsa kashe Edemawan saboda bashin da yake binta.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

An ruwaito cewa, budurwar ta bace ne tun a ranar 22 ga watan Disamba, 2022.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Sule Balarabe, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, Eyo na hannunsu a yanzu.

Ya ce, Eyo ya basu bayanan karya na cewa, budurwar ta sayar da wata kadararsa da kudinta ya kai kimanin Naira miliyan tara sannan kuma taki biyansa.

Sule, ya kara da cewa, Eyo ya yi hayar wasu mutane su sace ta don ya karbi kudinsa, amma aka kashe ta aka kuma boye gawarta a cikin tankin ruwan, inda ya ce, ana ci gaba da bincike don a kamo sauran mutanen da hada baki da su don hallaka budurwar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, ya ranci bashin budurwar har kimanin Naira miliyan 1.2 wacce kuma aka ce, yana yin soyayya da wata ‘yar uwarta mai suna Ruth Edem ‘yar shekara 22 kuma daliba a jami’ar UNICAL.

Wani dan uwan budurwar da bai bukaci a bayyana sunansa ba ya ce, Eyo ya ranci kudin budurwar kimanin Naira miliyan 1.2 a farkon wannan shekarar don bunkasa kasuwancinsa na sayar da manja.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

CMG Ya Yi Bitar Murnar Bikin Bazara Na 2023 Karo Na Farko

LABARAI MASU NASABA

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.