ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Manyan Kasa Ke Daukar Nauyin Ta’addanci – Ministan Ma’adanai

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
ta'addanci

Ministan Ma’adanai na Kasa, Dele Alake, ya ce Gwamnatin Tarayya ta gano cewa ‘yan Nijeriya masu karfin fada a ji ne da ke da hannu wajen hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba ke daukar nauyin ‘yan bindiga da ta’addanci a kasar nan.

Ya bayyana hakan ne a a lokacin da yake kare kasafin kudin shekarar 2024 a gaban Kwamitin Majalisar Wakilai Mai Kula da Ma’adanai cikin makon nan.

  • Dalilin Da Yasa Ta’addanci Ke Ci Gaba Duk Da Kasafin Kudi Mai Gwabi Da Sojoji Ke Samu – Shugaban Tsaro
  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD

Alake ya ce: “Wani binciken da muka gudanar ya yi nuni da cewa yawancin wannan rashin tsaro da ake fama da shi na ‘yan bindiga da ta’addanci yana da alaka da wannan bangare na masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.
“Wadannan da kuke zaton ba ma’aikatanku ba ne, ko kuke ganin kamar ba mutanen da suke hakar zinariya a kasa ba ne, lallai ya kamata ku fahimta cewa su ne, sannan kuma, ‘yan Nijeriya masu karfin ikon fada a ji ne ke daukar nauyinsu ba wasu ‘yan kasashen waje bane. “Eh, za ku iya ganin baki da aka ajiye a matsayin wasu alamu na basaja, amma ba su ne tushen asalin aikin ba, ‘yan Nijeriya ne masu isa da iko wadanda suke goyon bayan wadancan ‘yan kasashen waje da kuke gani a kan tituna suke aiwatar da hakan.

ADVERTISEMENT

“Wadanda ba su da karfi da suke aiki tare da masu aikin hakar ma’adinai, na basu damar kafa kungiyarsu ta hadin gwiwa domin kowane dan Nijeriya yana da hakkin rayuwa da bukatunsa, kuma idan har gwamnati ba za ta iya samar da wadannan abubuwa domin magance bukatu ba, to ba za mu iya ba da wannan shawara kuma mu tura ku cikin daji ba.”

Ya ce inganta tsaro a wuraren hakar ma’adanai da wuraren da ake son ya tabbata da kuma samar da aminci a fannin hakar ma’adinan kansa a Nijeriya zai dawo da masu zuba jari. Alake ya ce adadin ma’adanan da aka samar a Nijeriya ya haura Dala biliyan 700, inda ya ce kasar na da nau’in ma’adanai 44 da za a biya manyan bukatu, amma a halin yanzu ya zayyana guda bakwai kadai da suka zama mafi girman bukatu a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

Shugaban kwamitin, Gaza Gbefwi, ya ce bangaren ma’adanai mafiya karfi ya kasance babban fata na karshe ga Nijeriya na samun nasarar bunkasar tattalin arzikin da ake bukata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari
Kotu Da Ɗansanda

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Next Post
kiwon kaji

Masu Kiwon Kaji 103 Suka Amfana Da Taimakon Hukumar NALDA

LABARAI MASU NASABA

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.