• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Manyan Kasa Ke Daukar Nauyin Ta’addanci – Ministan Ma’adanai

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
ta'addanci

Ministan Ma’adanai na Kasa, Dele Alake, ya ce Gwamnatin Tarayya ta gano cewa ‘yan Nijeriya masu karfin fada a ji ne da ke da hannu wajen hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba ke daukar nauyin ‘yan bindiga da ta’addanci a kasar nan.

Ya bayyana hakan ne a a lokacin da yake kare kasafin kudin shekarar 2024 a gaban Kwamitin Majalisar Wakilai Mai Kula da Ma’adanai cikin makon nan.

  • Dalilin Da Yasa Ta’addanci Ke Ci Gaba Duk Da Kasafin Kudi Mai Gwabi Da Sojoji Ke Samu – Shugaban Tsaro
  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD

Alake ya ce: “Wani binciken da muka gudanar ya yi nuni da cewa yawancin wannan rashin tsaro da ake fama da shi na ‘yan bindiga da ta’addanci yana da alaka da wannan bangare na masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.
“Wadannan da kuke zaton ba ma’aikatanku ba ne, ko kuke ganin kamar ba mutanen da suke hakar zinariya a kasa ba ne, lallai ya kamata ku fahimta cewa su ne, sannan kuma, ‘yan Nijeriya masu karfin ikon fada a ji ne ke daukar nauyinsu ba wasu ‘yan kasashen waje bane. “Eh, za ku iya ganin baki da aka ajiye a matsayin wasu alamu na basaja, amma ba su ne tushen asalin aikin ba, ‘yan Nijeriya ne masu isa da iko wadanda suke goyon bayan wadancan ‘yan kasashen waje da kuke gani a kan tituna suke aiwatar da hakan.

“Wadanda ba su da karfi da suke aiki tare da masu aikin hakar ma’adinai, na basu damar kafa kungiyarsu ta hadin gwiwa domin kowane dan Nijeriya yana da hakkin rayuwa da bukatunsa, kuma idan har gwamnati ba za ta iya samar da wadannan abubuwa domin magance bukatu ba, to ba za mu iya ba da wannan shawara kuma mu tura ku cikin daji ba.”

Ya ce inganta tsaro a wuraren hakar ma’adanai da wuraren da ake son ya tabbata da kuma samar da aminci a fannin hakar ma’adinan kansa a Nijeriya zai dawo da masu zuba jari. Alake ya ce adadin ma’adanan da aka samar a Nijeriya ya haura Dala biliyan 700, inda ya ce kasar na da nau’in ma’adanai 44 da za a biya manyan bukatu, amma a halin yanzu ya zayyana guda bakwai kadai da suka zama mafi girman bukatu a duniya.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Shugaban kwamitin, Gaza Gbefwi, ya ce bangaren ma’adanai mafiya karfi ya kasance babban fata na karshe ga Nijeriya na samun nasarar bunkasar tattalin arzikin da ake bukata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
Next Post
kiwon kaji

Masu Kiwon Kaji 103 Suka Amfana Da Taimakon Hukumar NALDA

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.