• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Manyan Kasa Ke Daukar Nauyin Ta’addanci – Ministan Ma’adanai

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
ta'addanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Ma’adanai na Kasa, Dele Alake, ya ce Gwamnatin Tarayya ta gano cewa ‘yan Nijeriya masu karfin fada a ji ne da ke da hannu wajen hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba ke daukar nauyin ‘yan bindiga da ta’addanci a kasar nan.

Ya bayyana hakan ne a a lokacin da yake kare kasafin kudin shekarar 2024 a gaban Kwamitin Majalisar Wakilai Mai Kula da Ma’adanai cikin makon nan.

  • Dalilin Da Yasa Ta’addanci Ke Ci Gaba Duk Da Kasafin Kudi Mai Gwabi Da Sojoji Ke Samu – Shugaban Tsaro
  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD

Alake ya ce: “Wani binciken da muka gudanar ya yi nuni da cewa yawancin wannan rashin tsaro da ake fama da shi na ‘yan bindiga da ta’addanci yana da alaka da wannan bangare na masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.
“Wadannan da kuke zaton ba ma’aikatanku ba ne, ko kuke ganin kamar ba mutanen da suke hakar zinariya a kasa ba ne, lallai ya kamata ku fahimta cewa su ne, sannan kuma, ‘yan Nijeriya masu karfin ikon fada a ji ne ke daukar nauyinsu ba wasu ‘yan kasashen waje bane. “Eh, za ku iya ganin baki da aka ajiye a matsayin wasu alamu na basaja, amma ba su ne tushen asalin aikin ba, ‘yan Nijeriya ne masu isa da iko wadanda suke goyon bayan wadancan ‘yan kasashen waje da kuke gani a kan tituna suke aiwatar da hakan.

“Wadanda ba su da karfi da suke aiki tare da masu aikin hakar ma’adinai, na basu damar kafa kungiyarsu ta hadin gwiwa domin kowane dan Nijeriya yana da hakkin rayuwa da bukatunsa, kuma idan har gwamnati ba za ta iya samar da wadannan abubuwa domin magance bukatu ba, to ba za mu iya ba da wannan shawara kuma mu tura ku cikin daji ba.”

Ya ce inganta tsaro a wuraren hakar ma’adanai da wuraren da ake son ya tabbata da kuma samar da aminci a fannin hakar ma’adinan kansa a Nijeriya zai dawo da masu zuba jari. Alake ya ce adadin ma’adanan da aka samar a Nijeriya ya haura Dala biliyan 700, inda ya ce kasar na da nau’in ma’adanai 44 da za a biya manyan bukatu, amma a halin yanzu ya zayyana guda bakwai kadai da suka zama mafi girman bukatu a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Shugaban kwamitin, Gaza Gbefwi, ya ce bangaren ma’adanai mafiya karfi ya kasance babban fata na karshe ga Nijeriya na samun nasarar bunkasar tattalin arzikin da ake bukata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ta'addanciYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Cikin Gidan Jam’iyyar NNPP Na Kara Rincabewa A Kano

Next Post

Masu Kiwon Kaji 103 Suka Amfana Da Taimakon Hukumar NALDA

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 days ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

4 days ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

4 days ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

2 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

2 weeks ago
Next Post
kiwon kaji

Masu Kiwon Kaji 103 Suka Amfana Da Taimakon Hukumar NALDA

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.