• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

WHO Da UNICEF Za Su Yi Wa ‘Yan Mata Miliyan 7.7 Rigakafin Cutar Kansar Mahaifa A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
WHO

Nijeriya a hukumance ta shigar da allurar rigakafin cutar HPV a cikin tsarin rigakafinta na yau da kullum, da nufin kai wa yara mata miliyan 7.7 agaji cikin zagaye guda na allurar rigakafin cutar, wanda ya kasance mafi girman irinsa a yankin Afirka.

Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Muhammad Ali Pate, ya bayyana matukar damuwarsa kan cutar ta kansar mahaifa, yana mai cewa, “Asarar mata kusan 8,000 a duk shekara daga cutar da ake iya rigakafinta ba abu ne da za a amince da shi ba.“.

  • CMG Da WIPO Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa
  • Ganduje Ya Yaba Da Hukuncin Kotun Koli Akan Nasarar Zaben Tinubu

Pate ya jaddada cewa ceton rayuka da tabbatar da ingantaccen kiwon lafiya su ne jigon kudirin inganta lafiyar al’umma na shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ya kuma bayyana cewa, “A matsayina na uba, ni kaina, ina da ‘ya’ya mata hudu, dukkansu sun yi allurar rigakafin cutar HPV guda daya don kare su daga cutar kansar mahaifa.

“Ina so in yi kira ga ‘yan uwanmu iyaye da su tabbatar da cewa ‘yan matanmu sun amshi allurar rigakafin kamuwa da cutar kansar mahaifa”.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

‘Yan mata masu shekaru 9 zuwa 14 za su sami kashi ɗaya na maganin rigakafin na HPV, wanda yake da tasiri wajen hana kamuwa da cutar.

Daga nau’ukan maganin rigakafin akwai HPV 16 da 18.

Cutar kansar mahaifa ita ce ta biyu da take sanadin mutuwar mata masu shekaru 15 zuwa 44.

Wakilin WHO a Nijeriya, Dokta Walter Kazadi Mulombo, ya ce, “Wannan wani muhimmin lokaci ne a kokarin da Nijeriya ke yi na rage yawaitar kansar mahaifa – daya daga cikin cutar kansar da za a iya kawar da su ta hanyar alluran rigakafi.”

“Mun himmatu wajen tallafa wa gwamnati ta kara samun damar yin amfani da allurar rigakafin cutar ta HPV don kare lafiya da jin dadin rayuwar mata a nan da wasu shekaru masu zuwa.“.

UNICEF ta taka muhimmiyar rawa a wannan shiri, inda ta siyo rigakafin cutar ta HPV kusan miliyan 15 a madadin Gwamnatin Nijeriya. Bugu da kari, UNICEF ta samar da kayan fadakarwa da suka hada da radiyo da tallace-tallace na Talabijin a cikin harsunan gida da yawa don kawar da jita-jita game da rigakafin.

Taron kaddamar da shirin rigakafin na tsawon kwanaki biyar, ya kunshi makarantu da al’umma a fadin jihohi 16 da kuma Abuja.

A haka kuma, maganin zai zama wani ɓangare na tsarin rigakafi na yau da kullum a cibiyoyin kiwon lafiya.

Ana sa rai Kashi na biyu zai fara aiki a watan Mayun 2024, wanda zai ƙunshi jihohi 21.

Ana yin allurar rigakafin cutar HPV kyauta, wanda Ma’aikatar Kiwon Lafiya ta Tarayya, tare da tallafin Gidauniyar Gavi, the Vaccine Alliance, UNICEF, WHO, da sauran abokan haɗin gwiwa suka haɗa hannu suka samar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda 6, Sun Kwato AK-47 Da Babura A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.