• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Yi Wa EU Wankin Babban Bargo Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike ya yi wa Kungiyar Tarayyar Turai (EU) wankin babban bargo kan rahoton zaben shugaban kasa na 2023.

Ya ce rahoton bai bayar da hakikanin gaskiyar zaben da aka gudanar a kasar ba, amma ya haifar da mummunar fahimta a zukatan al’umma musamman a Jihar Ribas.

  • Nijeriya Na Fuskantar Karancin Alkalai
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Muhimmanta ‘Yancin ‘Yan Jarida – Minista

Wike ya nuna rashin jin dadinsa ne a lokacin da jakadan EU a NIjeriya, Samuela Isopi, ya kai masa ziyarar aiki a ofishinsa.

Ministan ya ce ya kamata Kungiyar EU ta kasance mai sa ido a zaben da ya gabata ba wai ta gabatar da wani rahoto da ba zai bayar da hakikanin tsarin dimokuradiyya a Nijeriya ba.

Tawagar masu sa ido a zaben na Kungiyar Tarayyar Turai (EUOM) ta bakin babban jami’inta, Barry Andres, a watan Yuni sun gabatar da rahotonsu na zaben Nijeriya da ya gabata, tare da bayyana wasu muhimman abubuwa guda shida da suka ba da shawarwari a kai.

LABARAI MASU NASABA

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

Wike, ya ce dokokin Nijeriya ba za su iya zama daidai da na EU ba saboda suna da yanayi daban-daban.

Ya ce: “Ban yarda da Tarayyar Turai kan rahoton zaben Nijeriya ba. Ya kamata su kasance masu saka ido ne. Dokokin Nijeriya ba za su iya zama daidai da dokokin EU ba saboda suna da yanayi mabambanta.

“A Jihar Ribas, rahoton EU ya bambanta da abin da ya faru a can. Ta yaya za a iya kwatanta mutanen da suka yi imani da dimokuradiyya kuma suke aiki da ita a matsayin mutanen da ba su fahimci dimokuradiyya ba?

“Damuwarmu ita ce yadda za mu inganta tattalin arzikin kasa, dole ne mu hada kai tare da cimma matsaya kan fannonin ci gaba a Babban Birnin Tarayya da ma kasar baki daya.”

Da take mayar da martani, jakadiyar Tarayyar Turai a Nijeriya, Samuela Isopi, ta ce masu sa ido masu zaman kansu ne suka hada rahoton kuma ba shi da alaka da ayyukanta.

Ta yi alkawarin yin aiki tare da ministan don bunkasa ci gaba a yankin Abuja da ma kasar gaba daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Labarai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
NAWIA
Labarai

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Next Post
Yadda Kwankwaso Da Abba Suka Jagoranci Auren Gatan Mutum 1,800 A Kano

Yadda Kwankwaso Da Abba Suka Jagoranci Auren Gatan Mutum 1,800 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.