ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Yi Wa EU Wankin Babban Bargo Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike ya yi wa Kungiyar Tarayyar Turai (EU) wankin babban bargo kan rahoton zaben shugaban kasa na 2023.

Ya ce rahoton bai bayar da hakikanin gaskiyar zaben da aka gudanar a kasar ba, amma ya haifar da mummunar fahimta a zukatan al’umma musamman a Jihar Ribas.

  • Nijeriya Na Fuskantar Karancin Alkalai
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Muhimmanta ‘Yancin ‘Yan Jarida – Minista

Wike ya nuna rashin jin dadinsa ne a lokacin da jakadan EU a NIjeriya, Samuela Isopi, ya kai masa ziyarar aiki a ofishinsa.

ADVERTISEMENT

Ministan ya ce ya kamata Kungiyar EU ta kasance mai sa ido a zaben da ya gabata ba wai ta gabatar da wani rahoto da ba zai bayar da hakikanin tsarin dimokuradiyya a Nijeriya ba.

Tawagar masu sa ido a zaben na Kungiyar Tarayyar Turai (EUOM) ta bakin babban jami’inta, Barry Andres, a watan Yuni sun gabatar da rahotonsu na zaben Nijeriya da ya gabata, tare da bayyana wasu muhimman abubuwa guda shida da suka ba da shawarwari a kai.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Wike, ya ce dokokin Nijeriya ba za su iya zama daidai da na EU ba saboda suna da yanayi daban-daban.

Ya ce: “Ban yarda da Tarayyar Turai kan rahoton zaben Nijeriya ba. Ya kamata su kasance masu saka ido ne. Dokokin Nijeriya ba za su iya zama daidai da dokokin EU ba saboda suna da yanayi mabambanta.

“A Jihar Ribas, rahoton EU ya bambanta da abin da ya faru a can. Ta yaya za a iya kwatanta mutanen da suka yi imani da dimokuradiyya kuma suke aiki da ita a matsayin mutanen da ba su fahimci dimokuradiyya ba?

“Damuwarmu ita ce yadda za mu inganta tattalin arzikin kasa, dole ne mu hada kai tare da cimma matsaya kan fannonin ci gaba a Babban Birnin Tarayya da ma kasar baki daya.”

Da take mayar da martani, jakadiyar Tarayyar Turai a Nijeriya, Samuela Isopi, ta ce masu sa ido masu zaman kansu ne suka hada rahoton kuma ba shi da alaka da ayyukanta.

Ta yi alkawarin yin aiki tare da ministan don bunkasa ci gaba a yankin Abuja da ma kasar gaba daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Yadda Kwankwaso Da Abba Suka Jagoranci Auren Gatan Mutum 1,800 A Kano

Yadda Kwankwaso Da Abba Suka Jagoranci Auren Gatan Mutum 1,800 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.