ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Karancin Alkalai

by Leadership Hausa
3 years ago
Alkalai

Bayanan da aka samu a ‘yan kwanakin nan na nuna akwai karancin alkalai da mayan ma’aikata musamman a manyan kotuna kassar nan, Kotun Koli da Kotun Daukaka Kara.

Rahotanni sun bayyana cewa, karancin alkalai a Kotun Koli ya bayyana ne bayan ajiye aikin da Maishari’a Amina Adamu Augie, da Maishari’a Mary Odili wadda ta yi ritaya kafin ita da kuma rasuwar Maishari’a Centus Chima Nweze. Rahoton ya kuma nuna cewa, a halin yanzu alkalai 11 suka rage maimakon alkalai 21 da doka ta tanada. Wannan lamarin yana matukar nakasa ayyukan masu shari’a saboda yawan aikin da ke gaban su hakan kuma yana shafar kokarin su na sauke nauyin yanke hukunce-hukunce a shari’un da ke gaban su.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Agaji Bayan Da Ya Kai Musu Kudin Fansa A Kaduna
  • Jirgin Sojoji Ya Yi Wa ‘Yan Ta’adda Luguden Wuta A Zamfara

Karin matsalar kuma a nan shi ne a cikin alkalai 11 da suka rare a kotun kolin 7 daga cikin su za su shiga aikin sauraran daukaka karar da da ‘yan takarar shugabancin kasar nan Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da Peter Obi na jam’iyyar LP sai kuma jam’iyya APM wadanda suke kalubalantar nasarar da dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu a zaben da aka yi a shekarar 2023 wanda kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa ta tabbatar masa da nasara kwanakin baya.

ADVERTISEMENT

Haka ya zama saura alkalai 4 kenan da za su fuskanci dinbin kararrakin da ke gaban Koton Kolin ciki har da kararrakin zaben gwamnoni wanda shi ma sai ya dangana da Koton Koli don yanke hukunci.

Hukumar Kula da Harkokin Shari’a (NJC) ce ke da alhakin amincewa da wadanda za a nada a matsayin alkalai a Koton Kolin daga na sai shugaban kasa ya mika sunayen su ga majalisar dattawa don su tabbatar da su, aikin su ne yanke hukunci a kan matsalolin da sukan taso a tsakanin gwamnatin tarayya da na jihohi da kuma matsalolin da ke tasowa a tsakanin jiha da jiha da sauran rikice-rikice a tsakanin al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Shugabanin manyan kotuna biyu na kasa sun koka a kan yadda aiki ya yi musu yawa da kuma karancin alkalai da za su fuskanci ayyukan. A jawabinsa kwanakin baya lokacin da ake rantsar da alkalai 9 da za su yi aiki a kotun daukaka kara, alkalain alkalan Nijeriya, Maishari’a Olukayode Ariwoola, ya koka a kan yadda shari’un zabe suka cika kotunanmu, ya ce, suna matukar takura alkalai, aikin kuma yana yi musu yawa kwarai da gaske, in ji shi.

A watan Nuwamba na shekarar da ta gabata, a yayin rantsar da sabbin manyan lauyoyi 62 na kasa a Abuja, alkalin alkalan Nijeriya Ariwoola ya jaddada cewa, bincdike ya nuna cewa Koton Kolin Nijeriya ce tafi duk wata kotun koli a duniya yawan ayyuka, wanan yana nuna irin aiki tukurun manyan alkalan Nijeriya.

A yayin da ake shari’u fiye da 6,884 kuma gashi alkalan da za su saurari wadanna shari’un suna kara raguwa, lallai za a iya samun matsalar dadewa shari’u, wanda kuma dadewar shari’a tamkar rashin aldalci ne ga masu neman hakkinsu.

Rahotanni sun nuna cewa a bayan zaben shekarar 2023 manyan kotunan tarayya sun karbi kararraki fiye da 3,000 wadanda ake sa ran za su bi ta kutunnan daukaka kara har zuwa Koton Koli don warwarewa.

Haka kuma shugabar kotun daukaka kara, Mai shari’a Dongban-Mensem, ta yi bayani kamar yadda alkalin alkalan Nijeriya ya yi a yayin kaddamar da shekarar shari’a ta 2023/2024.

Ta ce, kutun na da kararraki fiye da 39,526 wadanda suka rarraba a bangarorin kotun 20 sun kuma hada da kararrakin zabe. Maishari’a Dongban-Mensem ta bayyana cewa, bayan babban zaben 2023 sun kafa kotunan zabe 98 da za su duba shari’u 1,209 da ‘yan takarar zabe suka mika wa kotunan a jihohi daban daban.

Ta bayyana damuwar ta a kan yadda shari’un zabe suka cika kotunan Nijeriya wanda hakan na nufin cewa, sauran matsaloli da suka shafi rikice-rikicen filaye, hakokin dan adam, matsalar kasuwanci da sauran rikice-rikice za su ci gaba da zama a kotuna na tsawon lokaci.

Alkali alkalan Nijeriya, Ariwoola da shugabar kotun daukaka kara, Dongban-Mensen sun yi kira da cewa, bai kamata a ce dukkan shari’un zabe sai sun dangana ga kotuna ba, ya kamata a rinka neman hanyar warware rikice -rikicen zabe musamman ganin yadda kotuna suka cika da shari’u da ke bukatar a funskance su a kotunanmu.

Yana kuma da matukar muhimmanci a a kafa kotuna na musamman don sauraron kararrakin zabe kamar yadda kungiyar lauyoyi ta kasa ta yi kwanakin baya, a kan haka kuma muna kira ga Hukumar Kula da Harkokin Shari’a NJC ta mika sunayen wadanda ya kamata a nada a mastayin alkalan Koton Koli kamar yadda dokar kasa ta 230(1) (B) na kundin tsarin mulkin Nijeriya ya samar, ya kuma kamata a samar da isassun ma’aikata a kananan kotunan kasar nan don aiki a kan shari’un da ke gabansu kamar yadda ya kamata, kuma kan lokaci.

Alkalai
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Maulid

Tsoron Allah Da Ibadar Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.