ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

by Sadiq
1 year ago
Wutar Lantarki

Wani mutum mai suna Amas ya rasa ransa sakamakon makalewa da ya yi a jikin wayar wutar lantarki a unguwar Ekeki, kusa da hedikwatar ‘yansanda da ke kan titin Azikoro a Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa.

Marigayin dai ba ma’aikacin Kamfanin Power Holding Company of Nigeria (PHCN) ba ne, amma yana zaune ne a unguwar kuma yana hada wa mutane wuta.

  • 2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi
  • CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista

Mazauna yankin sun shaida wa manema labarai cewa, sakamakon rashin wutar lantarki da ake fama da shi a jihar, akasarin mutane sun gwammace hada wutar lantarki a kan layin gwamnatin tarayya wanda ake samun wutar lantarkin akalla sa’o’i 12 zuwa 13 a kullum.

ADVERTISEMENT

Marigayin dan asalin karamar hukumar Nembe a jihar ya rasu ya bar ‘ya’ya biyu, ya makale ne a kan wayar wutar lantarkin kafin jami’an kamfanin PHCN su sauko da shi.

Wani mazaunin Azikoro mai suna Micheal Orubo wanda lamarin ya faru a kan idonsa, ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai saukin kai wanda yake aikin hada wutar lantarki domin kula da iyalinsa.

LABARAI MASU NASABA

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Ya ce, “Amas yana zaune a unguwarmu, kuma yana aikin hada wuta ne a yanki. Me ya sa mutuwa za ta zo masa a haka? Ya tafi ya bar mu ba zai sake dawowa ba.

“Yana da saukin kai, wa zai kula da yaran da ya bari. Kudin da yake samu a aikin hada wutar lantarki da shi yake amfani wajen ciyar da iyalinsa. Wace irin mutuwa ce wannan? Mutumin da muke tare tsawon lokacin da ake ruwan sama yanzu, ya tafi ne da nufin idan ruwa ya dauke ya gyara musu wuta.”

Wani mazaunin yankin ya ce, “Ya wuce ni bai wuce minti biyar ba. Ruwan sama yana tsayawa, sai ihun mutane muka jiyo, nan take muka garzaya wajen da lamarin ya faru amma ba za mu iya taimakonsa ba, saboda ya daure jikinsa da bel, don haka ya makale sosai a jikin falwaya, saboda duk mun tsorata kuma har yanzu ana ruwan sama.”

Ma’aikatan kamfanin wuta na PHCN, daga baya sun zo sauke gawar daga jikin falwayar da ya makale.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Musa Muhammed bai ce komai kan faruwar lamarin ba zuwa lokacin hada wannan rahoton.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
Manyan Labarai

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Next Post
RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.