• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

by Sadiq
12 months ago
in Labarai
0
Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani mutum mai suna Amas ya rasa ransa sakamakon makalewa da ya yi a jikin wayar wutar lantarki a unguwar Ekeki, kusa da hedikwatar ‘yansanda da ke kan titin Azikoro a Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa.

Marigayin dai ba ma’aikacin Kamfanin Power Holding Company of Nigeria (PHCN) ba ne, amma yana zaune ne a unguwar kuma yana hada wa mutane wuta.

  • 2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi
  • CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista

Mazauna yankin sun shaida wa manema labarai cewa, sakamakon rashin wutar lantarki da ake fama da shi a jihar, akasarin mutane sun gwammace hada wutar lantarki a kan layin gwamnatin tarayya wanda ake samun wutar lantarkin akalla sa’o’i 12 zuwa 13 a kullum.

Marigayin dan asalin karamar hukumar Nembe a jihar ya rasu ya bar ‘ya’ya biyu, ya makale ne a kan wayar wutar lantarkin kafin jami’an kamfanin PHCN su sauko da shi.

Wani mazaunin Azikoro mai suna Micheal Orubo wanda lamarin ya faru a kan idonsa, ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai saukin kai wanda yake aikin hada wutar lantarki domin kula da iyalinsa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

Ya ce, “Amas yana zaune a unguwarmu, kuma yana aikin hada wuta ne a yanki. Me ya sa mutuwa za ta zo masa a haka? Ya tafi ya bar mu ba zai sake dawowa ba.

“Yana da saukin kai, wa zai kula da yaran da ya bari. Kudin da yake samu a aikin hada wutar lantarki da shi yake amfani wajen ciyar da iyalinsa. Wace irin mutuwa ce wannan? Mutumin da muke tare tsawon lokacin da ake ruwan sama yanzu, ya tafi ne da nufin idan ruwa ya dauke ya gyara musu wuta.”

Wani mazaunin yankin ya ce, “Ya wuce ni bai wuce minti biyar ba. Ruwan sama yana tsayawa, sai ihun mutane muka jiyo, nan take muka garzaya wajen da lamarin ya faru amma ba za mu iya taimakonsa ba, saboda ya daure jikinsa da bel, don haka ya makale sosai a jikin falwaya, saboda duk mun tsorata kuma har yanzu ana ruwan sama.”

Ma’aikatan kamfanin wuta na PHCN, daga baya sun zo sauke gawar daga jikin falwayar da ya makale.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Musa Muhammed bai ce komai kan faruwar lamarin ba zuwa lokacin hada wannan rahoton.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjaliBayelsaFalwayaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

Next Post

RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

Related

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

14 minutes ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

2 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

3 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

4 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

5 hours ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

6 hours ago
Next Post
RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
ÆŠan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

ÆŠan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.