• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

by CMG Hausa
3 years ago

Da safiyar yau Talata ne aka bude zaman farko na taron kolin G20, a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron, ya kuma gabatar da jawabi.

A jawabin nasa Xi Jinping ya ce, a halin yanzu, ana fuskantar babban kalubalen raya kasashen duniya. Don haka ya kamata mambobin G20 su sauke nauyin dake bisa wuyansu a matsayinsu na manyan kasashen duniya, domin neman bunkasuwar kasa da kasa, da tallafawa alummun duniya, yayin da ake tabbatar da ci gaban duniya baki daya.

  • Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand

Ya kuma kara da cewa, a halin yanzu, kasashen duniya, musamman ma kasashe masu tasowa suna fuskantar kalubalen raguwar tattalin arziki. Don haka ya ba da shawarar kafa dangantakar abokantaka ta neman farfado da tattalin arzikin duniya, da mai da aikin neman ci gaba, da raya alumma a matsayin babban aikin da aka sanya gaba, tare da mai da hankali kan bukatun kasashe maso tasowa.

Kaza lika ya ce kasar Sin tana goyon bayan shigar da kungiyar tarayyar kasashen Afirka wato AU kungiyar G20.

Haka kuma, cikin jawabinsa, shugaba Xi ya bayyana cewa, a halin yanzu, ya kamata a nemi ci gaban da kowace kasa za ta iya cin gajiya. Ci gaban da kowace kasa za ta ci gajiya tare, hakikanin ci gaba ne da ake bukata. Ya kamata kasashen dake kan gaba wajen samun ci gaba, su ba da taimako yadda ya kamata ga sauran kasashe, da kuma samar musu karin damammakin da suke bukata.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

Ya ce, Kalubaloli masu tsanani da ake fuskanta wajen neman bunkasuwar kasashen duniya, su ne babu isashen hatsi da makamashi.

Kuma, muhimmiyar hanyar da za mu yi amfani da ita wajen shawo kan wadannan kalubaloli ita ce, yin hadin gwiwa kan aikin sa ido a kasuwanni, da kuma kafa manyan kasuwannin bude kofa ga waje, domin karfafa tsarin samar da kayayyaki cikin hadin gwiwa, da kuma daidaita farashin kayayyaki yadda ya kamata.

Bugu da kari, Xi Jinping ya ce, a yayin babban taron wakilan Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin karo na 20 da aka yi watan jiya, an tabbatar da burin ci gaban kasar Sin da na JKS cikin shekaru 5 masu zuwa.

Kuma kasar Sin za ta tsaya tsayin daka wajen neman bunkasuwa cikin lumana, da zurfafa aikin kwaskwarima, da kuma kara bude kofa ga waje, domin neman farfadowar kasar Sin baki daya ta hanyar zamanintar da kasar. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Next Post
Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

LABARAI MASU NASABA

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.