• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Talata ne aka bude zaman farko na taron kolin G20, a tsibirin Bali na kasar Indonesiya, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron, ya kuma gabatar da jawabi.

A jawabin nasa Xi Jinping ya ce, a halin yanzu, ana fuskantar babban kalubalen raya kasashen duniya. Don haka ya kamata mambobin G20 su sauke nauyin dake bisa wuyansu a matsayinsu na manyan kasashen duniya, domin neman bunkasuwar kasa da kasa, da tallafawa alummun duniya, yayin da ake tabbatar da ci gaban duniya baki daya.

  • Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand

Ya kuma kara da cewa, a halin yanzu, kasashen duniya, musamman ma kasashe masu tasowa suna fuskantar kalubalen raguwar tattalin arziki. Don haka ya ba da shawarar kafa dangantakar abokantaka ta neman farfado da tattalin arzikin duniya, da mai da aikin neman ci gaba, da raya alumma a matsayin babban aikin da aka sanya gaba, tare da mai da hankali kan bukatun kasashe maso tasowa.

Kaza lika ya ce kasar Sin tana goyon bayan shigar da kungiyar tarayyar kasashen Afirka wato AU kungiyar G20.

Haka kuma, cikin jawabinsa, shugaba Xi ya bayyana cewa, a halin yanzu, ya kamata a nemi ci gaban da kowace kasa za ta iya cin gajiya. Ci gaban da kowace kasa za ta ci gajiya tare, hakikanin ci gaba ne da ake bukata. Ya kamata kasashen dake kan gaba wajen samun ci gaba, su ba da taimako yadda ya kamata ga sauran kasashe, da kuma samar musu karin damammakin da suke bukata.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Ya ce, Kalubaloli masu tsanani da ake fuskanta wajen neman bunkasuwar kasashen duniya, su ne babu isashen hatsi da makamashi.

Kuma, muhimmiyar hanyar da za mu yi amfani da ita wajen shawo kan wadannan kalubaloli ita ce, yin hadin gwiwa kan aikin sa ido a kasuwanni, da kuma kafa manyan kasuwannin bude kofa ga waje, domin karfafa tsarin samar da kayayyaki cikin hadin gwiwa, da kuma daidaita farashin kayayyaki yadda ya kamata.

Bugu da kari, Xi Jinping ya ce, a yayin babban taron wakilan Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin karo na 20 da aka yi watan jiya, an tabbatar da burin ci gaban kasar Sin da na JKS cikin shekaru 5 masu zuwa.

Kuma kasar Sin za ta tsaya tsayin daka wajen neman bunkasuwa cikin lumana, da zurfafa aikin kwaskwarima, da kuma kara bude kofa ga waje, domin neman farfadowar kasar Sin baki daya ta hanyar zamanintar da kasar. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mambobin ASUU A Bauchi Sun Yi Zanga-zanga Kan Bukatunsu 

Next Post

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

6 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

7 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

8 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

9 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

10 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

11 hours ago
Next Post
Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.