ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

by Sulaiman
2 weeks ago
Xi

A safiyar yau Alhamis 4 ga wata a nan birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Faransa Emmanuel Macron, wanda ke ziyarar aiki a kasar Sin.

A yayin ganawar, Xi Jinping ya nuna cewa, kamata ya yi kasashen Sin da Faransa su sauke nauyin dake bisa wuyansu, da bin ra’ayin kasancewar bangarori da dama, kana da tsayawa kan matsayin daidai. A cewarsa, kasar Sin na son yin aiki tare da bangaren Faransa, don tsayawa kan tattaunawa bisa tushen zaman daidai-wa-daida, da bude kofa, da ma gudanar da hadin gwiwa, ta yadda dangantakar dake tsakanin kasashen biyu za ta samu ci gaba yadda ya kamata, bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a cikin shekaru 60 na sabon zagaye.

Baya ga haka kuma, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata ko da yaushe kasashen biyu su yi hangen nesa, da kare ’yancin kai bisa matsayinsu na manyan kasashe, da nuna fahimta, da goyon bayan juna kan muhimman batutuwan dake jawo hankulansu duka. Xi ya kara da cewa, kasashen Sin da Faransa, duka su kasance mambobi yayin kafuwar MDD, kana zaunannun kasashe membobin kwamitin sulhu na MDD, don haka ya kamata su kiyaye tsarin kasa da kasa dake mayar da MDD ginshiki, kuma bisa tushen dokokin kasa da kasa, da karfafa yin cudanya, da hadin kai a fannin warware rikici ta hanyar siyasa, da inganta zaman lafiya da zaman karko na duniya, kana da sa kaimi ga ayyukan kwaskwarima da nufin kyautata harkokin duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

A nasa bangaren, shugaba Macron ya bayyana cewa, har kullum Faransa da Sin suna yin mu’amala sosai tsakanin shugabanninsu, kuma suna nuna amincewa da girmama juna. Kazalika kasarsa na dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakaninta da kasar ta Sin, tana kuma tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, tana mai fatan zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkannin fannoni tsakanin kasashen biyu.

Bayan shawarwarin, sun halarci bikin sanya hannu kan wasu takardun hadin kai da dama, da suka shafi makamashin nukiliya, da hatsi, da ilmi, da ma muhallin halittu da dai sauransu a tsakanin kasashensu biyu.

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

Baya ga haka, shugabannin kasashen biyu sun gana da manema labaru na Sin da kasashen waje tare, inda baki daya suka amince da karfafa amincewa juna, da habaka hakikanin hadin kai, da kara yin cudanyar al’adu, da kuma inganta yin kwaskwarima don kyautata ayyukan gudanar da harkokin duniya.

Kafin shawarwarin, shugaba Xi Jinping da uwar gidansa madam Peng Liyuan, sun shiryawa Macron da uwar gidansa Brigitte Macron bikin maraba da zuwansu. Har ila yau, da tsakar ranar yau Alhamis shugaba Xi Jinping da Peng Liyuan sun shiryawa Macron da Brigitte liyafar maraba.

Hakazalika, shugabannin biyu sun halarci bikin rufe taro na bakwai na kwamitin mamallaka masana’antu na kasashen Sin da Faransa, tare kuma da gabatar da jawabai. (Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.