ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

by Sulaiman
6 months ago
Xi

A safiyar yau Alhamis 4 ga wata a nan birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Faransa Emmanuel Macron, wanda ke ziyarar aiki a kasar Sin.

A yayin ganawar, Xi Jinping ya nuna cewa, kamata ya yi kasashen Sin da Faransa su sauke nauyin dake bisa wuyansu, da bin ra’ayin kasancewar bangarori da dama, kana da tsayawa kan matsayin daidai. A cewarsa, kasar Sin na son yin aiki tare da bangaren Faransa, don tsayawa kan tattaunawa bisa tushen zaman daidai-wa-daida, da bude kofa, da ma gudanar da hadin gwiwa, ta yadda dangantakar dake tsakanin kasashen biyu za ta samu ci gaba yadda ya kamata, bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a cikin shekaru 60 na sabon zagaye.

Baya ga haka kuma, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata ko da yaushe kasashen biyu su yi hangen nesa, da kare ’yancin kai bisa matsayinsu na manyan kasashe, da nuna fahimta, da goyon bayan juna kan muhimman batutuwan dake jawo hankulansu duka. Xi ya kara da cewa, kasashen Sin da Faransa, duka su kasance mambobi yayin kafuwar MDD, kana zaunannun kasashe membobin kwamitin sulhu na MDD, don haka ya kamata su kiyaye tsarin kasa da kasa dake mayar da MDD ginshiki, kuma bisa tushen dokokin kasa da kasa, da karfafa yin cudanya, da hadin kai a fannin warware rikici ta hanyar siyasa, da inganta zaman lafiya da zaman karko na duniya, kana da sa kaimi ga ayyukan kwaskwarima da nufin kyautata harkokin duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

A nasa bangaren, shugaba Macron ya bayyana cewa, har kullum Faransa da Sin suna yin mu’amala sosai tsakanin shugabanninsu, kuma suna nuna amincewa da girmama juna. Kazalika kasarsa na dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakaninta da kasar ta Sin, tana kuma tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, tana mai fatan zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkannin fannoni tsakanin kasashen biyu.

Bayan shawarwarin, sun halarci bikin sanya hannu kan wasu takardun hadin kai da dama, da suka shafi makamashin nukiliya, da hatsi, da ilmi, da ma muhallin halittu da dai sauransu a tsakanin kasashensu biyu.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Baya ga haka, shugabannin kasashen biyu sun gana da manema labaru na Sin da kasashen waje tare, inda baki daya suka amince da karfafa amincewa juna, da habaka hakikanin hadin kai, da kara yin cudanyar al’adu, da kuma inganta yin kwaskwarima don kyautata ayyukan gudanar da harkokin duniya.

Kafin shawarwarin, shugaba Xi Jinping da uwar gidansa madam Peng Liyuan, sun shiryawa Macron da uwar gidansa Brigitte Macron bikin maraba da zuwansu. Har ila yau, da tsakar ranar yau Alhamis shugaba Xi Jinping da Peng Liyuan sun shiryawa Macron da Brigitte liyafar maraba.

Hakazalika, shugabannin biyu sun halarci bikin rufe taro na bakwai na kwamitin mamallaka masana’antu na kasashen Sin da Faransa, tare kuma da gabatar da jawabai. (Bilkisu Xin)

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.