ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

by Sulaiman
9 months ago
Xi

A safiyar yau Alhamis 4 ga wata a nan birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Faransa Emmanuel Macron, wanda ke ziyarar aiki a kasar Sin.

A yayin ganawar, Xi Jinping ya nuna cewa, kamata ya yi kasashen Sin da Faransa su sauke nauyin dake bisa wuyansu, da bin ra’ayin kasancewar bangarori da dama, kana da tsayawa kan matsayin daidai. A cewarsa, kasar Sin na son yin aiki tare da bangaren Faransa, don tsayawa kan tattaunawa bisa tushen zaman daidai-wa-daida, da bude kofa, da ma gudanar da hadin gwiwa, ta yadda dangantakar dake tsakanin kasashen biyu za ta samu ci gaba yadda ya kamata, bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a cikin shekaru 60 na sabon zagaye.

Baya ga haka kuma, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata ko da yaushe kasashen biyu su yi hangen nesa, da kare ’yancin kai bisa matsayinsu na manyan kasashe, da nuna fahimta, da goyon bayan juna kan muhimman batutuwan dake jawo hankulansu duka. Xi ya kara da cewa, kasashen Sin da Faransa, duka su kasance mambobi yayin kafuwar MDD, kana zaunannun kasashe membobin kwamitin sulhu na MDD, don haka ya kamata su kiyaye tsarin kasa da kasa dake mayar da MDD ginshiki, kuma bisa tushen dokokin kasa da kasa, da karfafa yin cudanya, da hadin kai a fannin warware rikici ta hanyar siyasa, da inganta zaman lafiya da zaman karko na duniya, kana da sa kaimi ga ayyukan kwaskwarima da nufin kyautata harkokin duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

A nasa bangaren, shugaba Macron ya bayyana cewa, har kullum Faransa da Sin suna yin mu’amala sosai tsakanin shugabanninsu, kuma suna nuna amincewa da girmama juna. Kazalika kasarsa na dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakaninta da kasar ta Sin, tana kuma tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, tana mai fatan zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkannin fannoni tsakanin kasashen biyu.

Bayan shawarwarin, sun halarci bikin sanya hannu kan wasu takardun hadin kai da dama, da suka shafi makamashin nukiliya, da hatsi, da ilmi, da ma muhallin halittu da dai sauransu a tsakanin kasashensu biyu.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Baya ga haka, shugabannin kasashen biyu sun gana da manema labaru na Sin da kasashen waje tare, inda baki daya suka amince da karfafa amincewa juna, da habaka hakikanin hadin kai, da kara yin cudanyar al’adu, da kuma inganta yin kwaskwarima don kyautata ayyukan gudanar da harkokin duniya.

Kafin shawarwarin, shugaba Xi Jinping da uwar gidansa madam Peng Liyuan, sun shiryawa Macron da uwar gidansa Brigitte Macron bikin maraba da zuwansu. Har ila yau, da tsakar ranar yau Alhamis shugaba Xi Jinping da Peng Liyuan sun shiryawa Macron da Brigitte liyafar maraba.

Hakazalika, shugabannin biyu sun halarci bikin rufe taro na bakwai na kwamitin mamallaka masana’antu na kasashen Sin da Faransa, tare kuma da gabatar da jawabai. (Bilkisu Xin)

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.