ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Faransa 

by Sulaiman
7 months ago
Xi

A safiyar yau Alhamis 4 ga wata a nan birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Faransa Emmanuel Macron, wanda ke ziyarar aiki a kasar Sin.

A yayin ganawar, Xi Jinping ya nuna cewa, kamata ya yi kasashen Sin da Faransa su sauke nauyin dake bisa wuyansu, da bin ra’ayin kasancewar bangarori da dama, kana da tsayawa kan matsayin daidai. A cewarsa, kasar Sin na son yin aiki tare da bangaren Faransa, don tsayawa kan tattaunawa bisa tushen zaman daidai-wa-daida, da bude kofa, da ma gudanar da hadin gwiwa, ta yadda dangantakar dake tsakanin kasashen biyu za ta samu ci gaba yadda ya kamata, bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a cikin shekaru 60 na sabon zagaye.

Baya ga haka kuma, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata ko da yaushe kasashen biyu su yi hangen nesa, da kare ’yancin kai bisa matsayinsu na manyan kasashe, da nuna fahimta, da goyon bayan juna kan muhimman batutuwan dake jawo hankulansu duka. Xi ya kara da cewa, kasashen Sin da Faransa, duka su kasance mambobi yayin kafuwar MDD, kana zaunannun kasashe membobin kwamitin sulhu na MDD, don haka ya kamata su kiyaye tsarin kasa da kasa dake mayar da MDD ginshiki, kuma bisa tushen dokokin kasa da kasa, da karfafa yin cudanya, da hadin kai a fannin warware rikici ta hanyar siyasa, da inganta zaman lafiya da zaman karko na duniya, kana da sa kaimi ga ayyukan kwaskwarima da nufin kyautata harkokin duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

A nasa bangaren, shugaba Macron ya bayyana cewa, har kullum Faransa da Sin suna yin mu’amala sosai tsakanin shugabanninsu, kuma suna nuna amincewa da girmama juna. Kazalika kasarsa na dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakaninta da kasar ta Sin, tana kuma tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, tana mai fatan zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkannin fannoni tsakanin kasashen biyu.

Bayan shawarwarin, sun halarci bikin sanya hannu kan wasu takardun hadin kai da dama, da suka shafi makamashin nukiliya, da hatsi, da ilmi, da ma muhallin halittu da dai sauransu a tsakanin kasashensu biyu.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Baya ga haka, shugabannin kasashen biyu sun gana da manema labaru na Sin da kasashen waje tare, inda baki daya suka amince da karfafa amincewa juna, da habaka hakikanin hadin kai, da kara yin cudanyar al’adu, da kuma inganta yin kwaskwarima don kyautata ayyukan gudanar da harkokin duniya.

Kafin shawarwarin, shugaba Xi Jinping da uwar gidansa madam Peng Liyuan, sun shiryawa Macron da uwar gidansa Brigitte Macron bikin maraba da zuwansu. Har ila yau, da tsakar ranar yau Alhamis shugaba Xi Jinping da Peng Liyuan sun shiryawa Macron da Brigitte liyafar maraba.

Hakazalika, shugabannin biyu sun halarci bikin rufe taro na bakwai na kwamitin mamallaka masana’antu na kasashen Sin da Faransa, tare kuma da gabatar da jawabai. (Bilkisu Xin)

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861 Na 2026 Ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.