A ranar 13 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isar da sakon alhini ga takwaransa na Nijeriya Muhammadu Buhari, bisa abkuwar hadarin nutsewar jirgin ruwa da ya faru a kasar.
Xi Jinping ya ce, ya kadu da samun labarin hadarin da ya auku a jihar Anambra dake kasar Nijeriya, wanda ya haddasa rasuwar mutane da dama.
Don haka, a madadin gwamnatin kasar Sin da ma jama’arta, yana mika ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu sakamakon hadarin, tare da jajantawa iyalansu. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp