• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Kirkiro Da Ma’aikatar Kula Da Harkokin Fulani – Bello Badejo

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Fulani

Shugaban Kungiyar Miyetti Allah Kyautal Hore na Kasa, Abdullahi Bello Badejo ya bayyana cewa ya kamata gwamnatin tarayya ta samar da ma’aikatar kula da harkokin Fulani.

Shugban ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kamma wani da taro da ya shafi Fulani mai taken ‘Fulani ina mafita.’
Ya ce taron yana da matukar muhimmanci a al’amuran da suka shafi Fulani, kuma taron ya gudana ne har kashi biyu.

  • NNPP Ta Yi Sabbin Kamu A Jihar Kaduna

A cewarsa, Fulanin Nijeriya suna fuskanta matsaloli daban-daban, shi ya sa suka ga ya fi dacewa su nemi Fulani su nuna masu cewa suna tare da su dari bisa dari tare da nuna musu cewa lalle suna da shugabanci da kuma wakilci, domin kar su dauka ba su da shugabanci ko kuma wakilci.

Ya kara da cewa sun nemi masu ruwa da tsaki wanda suke da ilimin zamani daga cikin Fulani da masana kan kiwon dabbobi a Nijeriya wadanda aka yi su shekaru da suka gabata, domin su bayar da shawarwari kan matsalolin da suka shafi Fulani a Nijeriya.

Ya nuna farin cikinsa bisa amsar goron gayyata na masu ruwa da tsaki kuma har sun tofa albarkacin bakinsu a wurin wannan taro.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

GORON JUMA’A

Shugaban kungiyar ya ce babu wani da zai kasance shugaba ko sarki ya ji dadi ana rikici a jiharsa ko yankinsa.
Ya ce, “Wannan shi ya sa muke ganin wasu gwamnoni ba laifinsu ba ne kuma shi ma shugaban kasa ba laifinsa ba ne ake ta rigima, musamman ta Fulani da wasu kabilu, domin gwamnati tana da fadi.

“Mu a kungiyan Miyetti Allah Kautal Hore ya za mu yi mu shigo domin taimaka wa gwamnati da kuma hukumomin tsaro wajen dakile rikici a tsakanin Fulani da sauran kabilu.

“Mun tara Fulani fiye da 14,000 wadanda suka hada da matasa maza da mata, muna tare da su domin yi musu gargadi da nuna masu muhimmancin zaman lafiya. Kuma cikin ikon Allah ina tsammanin za a samu nasara cikin abin da muke niyyar aiwatarwa,” in ji shi.
Ya ce wannan shi ne taro na farko wanda aka tara Fulanin Nijeriya da na kasashen Afirka saboda ana kan hanya kuma kwalliya za ta biya kudin sabulu.

Ya ce sun mika bukatar a kafa ma’aikata ta kulawa da harkokin da suka shafi Fulani kamar irin wadda take kulawa da harkokin da suka shafi Neja Delta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita
Al'adu

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

September 2, 2025
GORON JUMA’A
Goron Juma'a

GORON JUMA’A

August 15, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Next Post
Wuraren Shakatawa 10 Da Suka Fi Tasiri A Duniya (zamantakewa)

Wuraren Shakatawa 10 Da Suka Fi Tasiri A Duniya (zamantakewa)

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.