ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Kirkiro Da Ma’aikatar Kula Da Harkokin Fulani – Bello Badejo

by Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
Fulani

Shugaban Kungiyar Miyetti Allah Kyautal Hore na Kasa, Abdullahi Bello Badejo ya bayyana cewa ya kamata gwamnatin tarayya ta samar da ma’aikatar kula da harkokin Fulani.

Shugban ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kamma wani da taro da ya shafi Fulani mai taken ‘Fulani ina mafita.’
Ya ce taron yana da matukar muhimmanci a al’amuran da suka shafi Fulani, kuma taron ya gudana ne har kashi biyu.

  • NNPP Ta Yi Sabbin Kamu A Jihar Kaduna

A cewarsa, Fulanin Nijeriya suna fuskanta matsaloli daban-daban, shi ya sa suka ga ya fi dacewa su nemi Fulani su nuna masu cewa suna tare da su dari bisa dari tare da nuna musu cewa lalle suna da shugabanci da kuma wakilci, domin kar su dauka ba su da shugabanci ko kuma wakilci.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa sun nemi masu ruwa da tsaki wanda suke da ilimin zamani daga cikin Fulani da masana kan kiwon dabbobi a Nijeriya wadanda aka yi su shekaru da suka gabata, domin su bayar da shawarwari kan matsalolin da suka shafi Fulani a Nijeriya.

Ya nuna farin cikinsa bisa amsar goron gayyata na masu ruwa da tsaki kuma har sun tofa albarkacin bakinsu a wurin wannan taro.

LABARAI MASU NASABA

Goron Juma’a

GORON JUMA’A 22-05-2026

Shugaban kungiyar ya ce babu wani da zai kasance shugaba ko sarki ya ji dadi ana rikici a jiharsa ko yankinsa.
Ya ce, “Wannan shi ya sa muke ganin wasu gwamnoni ba laifinsu ba ne kuma shi ma shugaban kasa ba laifinsa ba ne ake ta rigima, musamman ta Fulani da wasu kabilu, domin gwamnati tana da fadi.

“Mu a kungiyan Miyetti Allah Kautal Hore ya za mu yi mu shigo domin taimaka wa gwamnati da kuma hukumomin tsaro wajen dakile rikici a tsakanin Fulani da sauran kabilu.

“Mun tara Fulani fiye da 14,000 wadanda suka hada da matasa maza da mata, muna tare da su domin yi musu gargadi da nuna masu muhimmancin zaman lafiya. Kuma cikin ikon Allah ina tsammanin za a samu nasara cikin abin da muke niyyar aiwatarwa,” in ji shi.
Ya ce wannan shi ne taro na farko wanda aka tara Fulanin Nijeriya da na kasashen Afirka saboda ana kan hanya kuma kwalliya za ta biya kudin sabulu.

Ya ce sun mika bukatar a kafa ma’aikata ta kulawa da harkokin da suka shafi Fulani kamar irin wadda take kulawa da harkokin da suka shafi Neja Delta.

Fulani
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

GORON JUMA’A 17-04-2026
Goron Juma'a

Goron Juma’a

June 5, 2026
GORON JUMA’A 01-07-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 22-05-2026

May 22, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
Labarai

Ku Kula Da Kyawawan Ɗabi’u, Su Ne Waɗanda Annabi SAW Ya Kira Duk Halitta A Kansu

April 17, 2026
Next Post
Wuraren Shakatawa 10 Da Suka Fi Tasiri A Duniya (zamantakewa)

Wuraren Shakatawa 10 Da Suka Fi Tasiri A Duniya (zamantakewa)

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.