• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Uwargida Za Ta Yi Mu’amula Da Uwar Mijin Da Zama Ya Hada Su?

by Amina Usman
2 years ago
in Zamantakewa
0
Ya Uwargida Za Ta Yi Mu’amula Da Uwar Mijin Da Zama Ya Hada Su?

Pensive African American young woman look in distance thinking pondering, thoughtful biracial millennial female lost in thoughts, suffer from depression or miscarriage, psychological help concept

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zamantakewa mu’amula ce da ke faruwa tsakanin mutane daban-daban. In aka ce zama ya hada ka da mutum to fa dole ka kasance mai abu biyu, Hakuri da Kauda kai.

Zama na aure zama ne da yake kunshe da kalubale mai dadi ko akasin haka, musamman in aka ce zama ya hada ka da uwa ko kuma wani dangi na miji. Da yawa mata suna daukan zama da uwar miji a matsayin wani zama mai tattara da kalubale wanda abun ba haka yake ba.

  • Cutar Shakewar Numfashi Ta Kashe Mutum 25 A Jihar Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Raunata Wasu A Katsina

Idan uwargida ta tsinci kanta a cikin matan da zama da uwar miji ya hada su to fa dole sai kin karo biyayya a kan wanda kike da shi, in aka ce biyayya ina nufin yanda uwargida za ta kalli mahaifanta haka ya kamata ta girmama na mijinta, yadda za ta yiwa iyayenta ladabi to su ma fa haka za ta yi musu.

Sannan uwargida ta kasance mai ihsani da kyautatawa tsakanin ta da uwar miji, idan uwar mijin na cin goro ta lazamci siya ta bata. Haka turare na jiki da na daki shi ma ta dan dinga siya tana ba ta ko ba kullum ba ko a wata sau daya.

Uwargida kar ki taba yarda ku raba tukunya da uwar mijinki, saboda yin haka yana kawo rabuwan kai sosai, in dai zaman gida ya hada uwsargida da sirika to ki daure ki kasance kina dafa abinci duka gida kuma kar ki kasance mai rowa ki zuba mata adadin da kika san zai ishe ta har ma wani bako ya zo ya ci, saboda yin hakan yana kara wa uwargida daraja da kima a idon sirikar ta da ma idon duniya baki daya. Kuma ko zaginta uwar mijin ta ji ana yi za ta so ta kare ta.

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar Tsofaffin ÆŠaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Uwargida ta kasance mai kauda kai ga abinda surukarta za ta yi ko ta ki yi. Kar uwargida ta ga an yi baki sun shige daki ta kwallafa rai sai ta kasa kunne ta ji me ake fada, ko kila tadinta ake yi, kar ki sake kiyi wannan za ki jiyo wa kanki abin da zai hana ki kwanciyar hankali, tun farko ma uwargida kar ta sa wa ranta wannan, ta sa wa zuciyar ta salama, ta sa wa ranta cewa in an yi baki a gidan to abin da ya dame su suke zantawa.

Kar uwargida ta kasance mai sa ido ga abinda Mijinta ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kasance mai kauda kai domin kuwa hakan zai kara mata daraja da kima a idon shi. Duk abin da zai kawo kar ki ce ke ma fa dole sai an miki a’a ki kauda kai in akwai rabonki sai ki ga ke ma an kawo miki. Kuma yin hakan yana kara wa uwargida daraja da kima a idon kowa ma ba miji kadai ba.

Aikace-Aikacen gida kar uwargida ta dauka zaman uwar mijinta a kusa da ita wata dama ce da za ta dinga saka uwar miji aiki ko kadan hakan ba tarbiyya ba ce kuma babu dan da zai ga haka ya ji dadi. Ko da ita ta nemi ta tayaki ki nuna mata ita uwa ce lokacin hutunta ne saboda haka ta je ta huta za ki yi aikin.

Nuna wa Maigida ya kyautata wa uwarsa kar uwargida ta jira wai sai dole miji ya yi wa uwarsa a’a ke ma kamar idonsa kike a gidan saboda haka ki nuna masa duk wasu hanyoyin kyautata wa mahaifiya, ki dinga nuna masa wanda hakan zai kara miki kima da daraja sosai a idonsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Uwar GidaUwar MijiiZama
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Next Post

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

Related

Kungiyar Tsofaffin ÆŠaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Ilimi

Kungiyar Tsofaffin ÆŠaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
Taskira

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

2 months ago
Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
Taskira

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

3 months ago
Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?
Taskira

Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?

4 months ago
Maganin Zubewar Mama Da Yadda Ake Gyara Shi 
Taskira

Yadda Mata Ke Daukar Yara Don Taya Su Aikin Gida

5 months ago
Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?
Taskira

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

9 months ago
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

LABARAI MASU NASABA

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.