• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

by Khalid Idris Doya
2 months ago
in Kananan Labarai
0
Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Bauchi ta bukaci al’ummomin Musulmi da Kiristoci mazauna unguwannin Yolan Bayara da ke cikin gundumar Miri da ke Bauchi da su kai zukatunsu nesa don samar da zaman lafiya tare da cewa har yanzu filin Makabarta da ake kokarin tada jijiyar wuya a kai har yanzu gwamnatin jihar ba ta bai wa kowa ko wata kungiyar ba.

LEADERSHIP HAUSA ta labarto cewa, rashin fahimtar ya samu asali ne sakamakon furucin da shugaban CAN a jihar Bauchi Rabaran Abraham Demius Damin ya yi na cewa gwamnatin jihar ta ba su fili mai girman kadada 50 domin su gina makabarta.

  • Musulmai Sun Fusata Da Matakin Gwamnatin Bauchi Kan Makabarta
  • Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan lamarin, Babban hadimin gwamnan Jihar kan hulda da ‘yan jarida da yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado, ya tabbatar da cewa, filin makabarta da aka takaddama akan sa, har ya zuwa wannan lokaci ba a bayar da shi wa wani ko kungiya ba.

Gidado wanda ke yana mayar da martani ne bisa koke da al’ummar Musulmi mazauna Yolan-Bayara suka yi a kwanakin baya dangane da wannan lamari, yana mai cewar, gwamnati takan bayar da filin kasa ne bisa bukatar da ta shafi al’umma.

Ya ce, “Abin da ke faruwa shi ne, Kungiyar Mabiya Addninin Kiristanci (CAN) ta rubuta wa gwamnati takarda tare da bukatar a ba su wani fili da za su mayar da shi makabartar mabiya addinin su a nan yankin Bayara dake cikin garin Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Ramadan: Fasto Ya Raba Wa Musulmi Kayan Masarufi A Kaduna

NIS Reshen Ribas Ta Kafa Kwamitin Bunkasa Walwalar Jami’ai

“Gwamnatin jiha ta bayar da umarnin a duba wani fili a farfajiyar wadannan al’ummai mai kimanin kadada hamsin (50) bisa dubi da cancantar a bai wa masu wadannan bukata bayan bibiyar dukkan ka’idoji na doka da suka dace da yin hakan, daga cikin babban filin da yake da murabba’in kadada 470 dake cikin wannan yanki na mazaunar wadannan al’ummai.

“Dangane da nazarce-nazarce da suka jibanci bayar da wannan fili da ake bukata, ya sa gwamnatin jiha ta kafa wani kwamiti a karkashin jagorancin mataimakin Gwamna, Sanata Baba Salihu Tela, hadi da wasu kwararru akan lamuran yin amfani da fili da safiyon sa, wadanda za su yi nazarin bayar da filin ga mabukata”.

Ya kwamitin da aka kafa zai yi nazarin duba wannan fili da ake bukata, tare da shawartar gwamnati bisa yin abin da ya dace, yana mai cewa, “Sai kwatsam al’ummar Musulmi na wannan gunduma suka rubuta wa gwamnati takardar koke da nunin cewa wannan fili na tasu al’umma ce”.

“Wannan fili da ake yin husuma akan sa, har zuwa wannan lokaci ba a bayar da shi wa kowa ba, domin har yanzu gwamnati tana cikin yin nazarin duba ka’idojin bayar da shi, kuma wajibi ne jama’a su san cewa a duk wani yanayi da gwamnati za ta bayar da filin kasa, walau wa daidaikun jama’a ne ko kungiyoyi, takan yi dubi da ka’idoji ne kamar yadda dokar fili ta zayyana, tare da yin nazarin diyya daya kamata a bai wa masu mallakar filin idan ya kasance na daidaikun jama’a ne ko al’umma”.

Mai bayar da shawara wa gwamna ya bayyana cewar, dukkan al’umman guda biyu, Musulmi da Kiristoci su na da ‘yancin neman fili daga wajen gwamnati domin bukatar samar da makabarta, sai sai ya ce sai an bi komai bisa ka’ida kafin.

Su dai al’ummar musulmi mazauna Yolan-Bayara sun gudana da wani taron manema labarai, inda suka nuna rashin gamsuwarsu bisa filin makabarta da suke kyautata zaton an bai wa al’ummar mabiya addinin kiristanci, su na masu cewar, wannan fili da aka bayar na kakanin-kakanin su ne.

Tawagar ta al’ummar Musulmi na Yolan Bayara ta gudanar da taron manema labaran ne a karkashin jagorancin Sani Sarki Yakubu wanda ya bayyana cewar, filin da suke yin magana akai na iyaye da kakanin su ne wanda a tuntuni ya kasance makabarta ce ta al’ummar Musulmi, wanda har ya zuwa wannan lokaci suke bunne mamatan su, don haka idan ya sake kasance wa makabartar mabiya addinin kiristanci, zai kasance ana tone mamatan Musulmi, ana musanyawa da mamatan ma’abutan wani addini, su na ganin yin hakan ba zai dadada wa kowane jinsin addini ba.

Yakubu ya ce ko kadan ba su adawa da bai wa kiristoci fili don su yi makabarta amma dai bai kamata a mallakar musu filin da tunin aka fara bisne musulmai a ciki ba.

“Su Kiristoci, ‘yan-wan mu ne maza da mata, kuma tare muke zaune shekaru aru-aru cikin kwanciyar hankali da lumana a tsakanin mu, don haka bamu kaunar wani sabani a tsakanin mu. Kuma mu masu biyayya ne wa gwamnati, kuma masu bin doka”, in ji jagora Sani Yakubu.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Uwargida Za Ta Yi Mu’amula Da Uwar Mijin Da Zama Ya Hada Su?

Next Post

Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara

Related

Ramadan: Fasto Ya Raba Wa Musulmi Kayan Masarufi A Kaduna
Kananan Labarai

Ramadan: Fasto Ya Raba Wa Musulmi Kayan Masarufi A Kaduna

3 days ago
NIS
Kananan Labarai

NIS Reshen Ribas Ta Kafa Kwamitin Bunkasa Walwalar Jami’ai

5 days ago
INEC Ta Kara Wa’adin Karbar Katin Zabe
Kananan Labarai

Zaben Gwamnoni: Ku Ankare Akwai Masu Shaidar Aikin Tsaro Ta Bogi, INEC Ga Masu Zabe

1 week ago
Shugabar Matan NNPP Reshen Abuja Ta ‘Yanta Fursunoni 4
Kananan Labarai

Shugabar Matan NNPP Reshen Abuja Ta ‘Yanta Fursunoni 4

1 month ago
Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil
Kananan Labarai

Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil

2 months ago
Tambuwal Ya Gabatar Da Kasafin Kudinsa Na Karshe a Sakkwato
Kananan Labarai

Tambuwal Ya Gabatar Da Kasafin Kudinsa Na Karshe a Sakkwato

4 months ago
Next Post
Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara

Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma'aikatun Sakkwato Da Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron CDF Na Bana

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron CDF Na Bana

March 27, 2023
Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.