ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamnatin

Gwamnatin Jihar Bauchi ta bukaci al’ummomin Musulmi da Kiristoci mazauna unguwannin Yolan Bayara da ke cikin gundumar Miri da ke Bauchi da su kai zukatunsu nesa don samar da zaman lafiya tare da cewa har yanzu filin Makabarta da ake kokarin tada jijiyar wuya a kai har yanzu gwamnatin jihar ba ta bai wa kowa ko wata kungiyar ba.

LEADERSHIP HAUSA ta labarto cewa, rashin fahimtar ya samu asali ne sakamakon furucin da shugaban CAN a jihar Bauchi Rabaran Abraham Demius Damin ya yi na cewa gwamnatin jihar ta ba su fili mai girman kadada 50 domin su gina makabarta.

  • Musulmai Sun Fusata Da Matakin Gwamnatin Bauchi Kan Makabarta
  • Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan lamarin, Babban hadimin gwamnan Jihar kan hulda da ‘yan jarida da yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado, ya tabbatar da cewa, filin makabarta da aka takaddama akan sa, har ya zuwa wannan lokaci ba a bayar da shi wa wani ko kungiya ba.

ADVERTISEMENT

Gidado wanda ke yana mayar da martani ne bisa koke da al’ummar Musulmi mazauna Yolan-Bayara suka yi a kwanakin baya dangane da wannan lamari, yana mai cewar, gwamnati takan bayar da filin kasa ne bisa bukatar da ta shafi al’umma.

Ya ce, “Abin da ke faruwa shi ne, Kungiyar Mabiya Addninin Kiristanci (CAN) ta rubuta wa gwamnati takarda tare da bukatar a ba su wani fili da za su mayar da shi makabartar mabiya addinin su a nan yankin Bayara dake cikin garin Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

“Gwamnatin jiha ta bayar da umarnin a duba wani fili a farfajiyar wadannan al’ummai mai kimanin kadada hamsin (50) bisa dubi da cancantar a bai wa masu wadannan bukata bayan bibiyar dukkan ka’idoji na doka da suka dace da yin hakan, daga cikin babban filin da yake da murabba’in kadada 470 dake cikin wannan yanki na mazaunar wadannan al’ummai.

“Dangane da nazarce-nazarce da suka jibanci bayar da wannan fili da ake bukata, ya sa gwamnatin jiha ta kafa wani kwamiti a karkashin jagorancin mataimakin Gwamna, Sanata Baba Salihu Tela, hadi da wasu kwararru akan lamuran yin amfani da fili da safiyon sa, wadanda za su yi nazarin bayar da filin ga mabukata”.

Ya kwamitin da aka kafa zai yi nazarin duba wannan fili da ake bukata, tare da shawartar gwamnati bisa yin abin da ya dace, yana mai cewa, “Sai kwatsam al’ummar Musulmi na wannan gunduma suka rubuta wa gwamnati takardar koke da nunin cewa wannan fili na tasu al’umma ce”.

“Wannan fili da ake yin husuma akan sa, har zuwa wannan lokaci ba a bayar da shi wa kowa ba, domin har yanzu gwamnati tana cikin yin nazarin duba ka’idojin bayar da shi, kuma wajibi ne jama’a su san cewa a duk wani yanayi da gwamnati za ta bayar da filin kasa, walau wa daidaikun jama’a ne ko kungiyoyi, takan yi dubi da ka’idoji ne kamar yadda dokar fili ta zayyana, tare da yin nazarin diyya daya kamata a bai wa masu mallakar filin idan ya kasance na daidaikun jama’a ne ko al’umma”.

Mai bayar da shawara wa gwamna ya bayyana cewar, dukkan al’umman guda biyu, Musulmi da Kiristoci su na da ‘yancin neman fili daga wajen gwamnati domin bukatar samar da makabarta, sai sai ya ce sai an bi komai bisa ka’ida kafin.

Su dai al’ummar musulmi mazauna Yolan-Bayara sun gudana da wani taron manema labarai, inda suka nuna rashin gamsuwarsu bisa filin makabarta da suke kyautata zaton an bai wa al’ummar mabiya addinin kiristanci, su na masu cewar, wannan fili da aka bayar na kakanin-kakanin su ne.

Tawagar ta al’ummar Musulmi na Yolan Bayara ta gudanar da taron manema labaran ne a karkashin jagorancin Sani Sarki Yakubu wanda ya bayyana cewar, filin da suke yin magana akai na iyaye da kakanin su ne wanda a tuntuni ya kasance makabarta ce ta al’ummar Musulmi, wanda har ya zuwa wannan lokaci suke bunne mamatan su, don haka idan ya sake kasance wa makabartar mabiya addinin kiristanci, zai kasance ana tone mamatan Musulmi, ana musanyawa da mamatan ma’abutan wani addini, su na ganin yin hakan ba zai dadada wa kowane jinsin addini ba.

Yakubu ya ce ko kadan ba su adawa da bai wa kiristoci fili don su yi makabarta amma dai bai kamata a mallakar musu filin da tunin aka fara bisne musulmai a ciki ba.

“Su Kiristoci, ‘yan-wan mu ne maza da mata, kuma tare muke zaune shekaru aru-aru cikin kwanciyar hankali da lumana a tsakanin mu, don haka bamu kaunar wani sabani a tsakanin mu. Kuma mu masu biyayya ne wa gwamnati, kuma masu bin doka”, in ji jagora Sani Yakubu.

Gwamnatin
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
Kananan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

April 28, 2026
Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi
Kananan Labarai

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

April 28, 2026
Next Post
Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara

Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma'aikatun Sakkwato Da Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.