ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Gwamnatin

Gwamnatin Jihar Bauchi ta bukaci al’ummomin Musulmi da Kiristoci mazauna unguwannin Yolan Bayara da ke cikin gundumar Miri da ke Bauchi da su kai zukatunsu nesa don samar da zaman lafiya tare da cewa har yanzu filin Makabarta da ake kokarin tada jijiyar wuya a kai har yanzu gwamnatin jihar ba ta bai wa kowa ko wata kungiyar ba.

LEADERSHIP HAUSA ta labarto cewa, rashin fahimtar ya samu asali ne sakamakon furucin da shugaban CAN a jihar Bauchi Rabaran Abraham Demius Damin ya yi na cewa gwamnatin jihar ta ba su fili mai girman kadada 50 domin su gina makabarta.

  • Musulmai Sun Fusata Da Matakin Gwamnatin Bauchi Kan Makabarta
  • Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan lamarin, Babban hadimin gwamnan Jihar kan hulda da ‘yan jarida da yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado, ya tabbatar da cewa, filin makabarta da aka takaddama akan sa, har ya zuwa wannan lokaci ba a bayar da shi wa wani ko kungiya ba.

ADVERTISEMENT

Gidado wanda ke yana mayar da martani ne bisa koke da al’ummar Musulmi mazauna Yolan-Bayara suka yi a kwanakin baya dangane da wannan lamari, yana mai cewar, gwamnati takan bayar da filin kasa ne bisa bukatar da ta shafi al’umma.

Ya ce, “Abin da ke faruwa shi ne, Kungiyar Mabiya Addninin Kiristanci (CAN) ta rubuta wa gwamnati takarda tare da bukatar a ba su wani fili da za su mayar da shi makabartar mabiya addinin su a nan yankin Bayara dake cikin garin Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

“Gwamnatin jiha ta bayar da umarnin a duba wani fili a farfajiyar wadannan al’ummai mai kimanin kadada hamsin (50) bisa dubi da cancantar a bai wa masu wadannan bukata bayan bibiyar dukkan ka’idoji na doka da suka dace da yin hakan, daga cikin babban filin da yake da murabba’in kadada 470 dake cikin wannan yanki na mazaunar wadannan al’ummai.

“Dangane da nazarce-nazarce da suka jibanci bayar da wannan fili da ake bukata, ya sa gwamnatin jiha ta kafa wani kwamiti a karkashin jagorancin mataimakin Gwamna, Sanata Baba Salihu Tela, hadi da wasu kwararru akan lamuran yin amfani da fili da safiyon sa, wadanda za su yi nazarin bayar da filin ga mabukata”.

Ya kwamitin da aka kafa zai yi nazarin duba wannan fili da ake bukata, tare da shawartar gwamnati bisa yin abin da ya dace, yana mai cewa, “Sai kwatsam al’ummar Musulmi na wannan gunduma suka rubuta wa gwamnati takardar koke da nunin cewa wannan fili na tasu al’umma ce”.

“Wannan fili da ake yin husuma akan sa, har zuwa wannan lokaci ba a bayar da shi wa kowa ba, domin har yanzu gwamnati tana cikin yin nazarin duba ka’idojin bayar da shi, kuma wajibi ne jama’a su san cewa a duk wani yanayi da gwamnati za ta bayar da filin kasa, walau wa daidaikun jama’a ne ko kungiyoyi, takan yi dubi da ka’idoji ne kamar yadda dokar fili ta zayyana, tare da yin nazarin diyya daya kamata a bai wa masu mallakar filin idan ya kasance na daidaikun jama’a ne ko al’umma”.

Mai bayar da shawara wa gwamna ya bayyana cewar, dukkan al’umman guda biyu, Musulmi da Kiristoci su na da ‘yancin neman fili daga wajen gwamnati domin bukatar samar da makabarta, sai sai ya ce sai an bi komai bisa ka’ida kafin.

Su dai al’ummar musulmi mazauna Yolan-Bayara sun gudana da wani taron manema labarai, inda suka nuna rashin gamsuwarsu bisa filin makabarta da suke kyautata zaton an bai wa al’ummar mabiya addinin kiristanci, su na masu cewar, wannan fili da aka bayar na kakanin-kakanin su ne.

Tawagar ta al’ummar Musulmi na Yolan Bayara ta gudanar da taron manema labaran ne a karkashin jagorancin Sani Sarki Yakubu wanda ya bayyana cewar, filin da suke yin magana akai na iyaye da kakanin su ne wanda a tuntuni ya kasance makabarta ce ta al’ummar Musulmi, wanda har ya zuwa wannan lokaci suke bunne mamatan su, don haka idan ya sake kasance wa makabartar mabiya addinin kiristanci, zai kasance ana tone mamatan Musulmi, ana musanyawa da mamatan ma’abutan wani addini, su na ganin yin hakan ba zai dadada wa kowane jinsin addini ba.

Yakubu ya ce ko kadan ba su adawa da bai wa kiristoci fili don su yi makabarta amma dai bai kamata a mallakar musu filin da tunin aka fara bisne musulmai a ciki ba.

“Su Kiristoci, ‘yan-wan mu ne maza da mata, kuma tare muke zaune shekaru aru-aru cikin kwanciyar hankali da lumana a tsakanin mu, don haka bamu kaunar wani sabani a tsakanin mu. Kuma mu masu biyayya ne wa gwamnati, kuma masu bin doka”, in ji jagora Sani Yakubu.

Gwamnatin
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

MASU ALAKA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
Kananan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

April 28, 2026
Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi
Kananan Labarai

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

April 28, 2026
Next Post
Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara

Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma'aikatun Sakkwato Da Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026
Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

Asibitin Tafi Da Gidanka Na Jirgin Ruwan Sin Ya Nufi Kasashen Afrika Da Kudancin Asiya Domin Bayar Da Hidimomin Jin Kai

July 22, 2026
Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

Iran Ta Musanta Zargin Ɓoye Makaman Nukiliya A Dutsen Kolang

July 22, 2026
An Kafa Cibiyar Binciken Wayewar Kai Ta Duniya

An Kafa Cibiyar Binciken Wayewar Kai Ta Duniya

July 22, 2026
Kano

Gwamnatin Kano Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi

July 22, 2026
Yawan Man Fetur Da Gas Da Sin Ta Samar A 2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Man Fetur Da Gas Da Sin Ta Samar A 2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

July 22, 2026
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Uba Da ‘Yarsa Sun Mutu Bayan Faɗawa Rijiya A Kano

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.