• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Amurka Ta Hau Kujerar Na Ki Ya Yayaye Lullubin Munafurcinta

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Yadda Amurka Ta Hau Kujerar Na Ki Ya Yayaye Lullubin Munafurcinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Amurka ta sake hana Palasdinawa cimma burinsu na kafa kasarsu mai ’yancin kai.

A ranar 18 ga wata, a yayin da kwamitin sulhun MDD ke kada kuri’u a kan wani daftarin shiri game da bukatar Palasdinu ta zama mamba a MDD, kasar Amurka ta sake hawan kujerar na ki, kuma ita ce kasa kadai da ta kada kuri’ar nuna rashin amincewa. Idan ba a manta ba, tuni a yau shekaru 13 da suka wuce, Palasdinu ta mika rokon zama mamba a MDD, amma sakamakon yadda ita Amurka ta hana, ba a kai ga mika shi ga babban taron MDD ba.

  • Kusan 90% Na Masu Amsa Tambayoyin Duniya Sun Yaba Da Gudummawar Da Sin Ke Bayarwa Ga Bunkasuwar Duniya Irin Na Kiyaye Muhalli, A Cewar Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN
  • Yankin Kudancin Tekun Pasifik Ba Zai Zamo Dandalin Hamayyar Kasashe Masu Karfi Ba, In Ji Ministan Wajen Sin

Sai dai ko shugaban kasar Amurka ko sauran manyan jami’an kasar, sau tari ne suka bayyana goyon bayansu ga shirin samar da kasashe biyu a matsayin hanya daya tilo mai dorewa ta zaman lafiya ta tsakanin Palasdinu da Isra’ila. To, amma idan ba ta amince da kafa kasar Palasdinu mai ’yancin kanta ba, ina ne za a yi zancen “samar da kasashe biyu”.

Lallai amsa ita ce, zakin baki ba wani abu ba ne, amma kome shawara da za a yanke, dole ne ta amfana wa muradun kasar Amurka. Sanin kowa ne Amurka na da alaka ta kut da kut da Isra’ila ta fannoni daban daban, musamman ma a lokacin da Amurka ke dab da fara babban zaben kasar, ba za ta iya raba kai da Isra’ila ba. Idan Palasdinu ta kai ga zama mamba a MDD, za ta samu damar kara fito da muryarta a duniya tare da samun karin goyon baya, matakin da ka iya matsa wa Isra’ila, baya ga lalata muradun Amurka a yankin gabas ta tsakiya.

Rikici na ci gaba a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wanda yake ta haifar da mummunan tasiri ga sauran kasashen yankin. A cikin irin wannan hali, duk kasar da ke da niyyar tabbatar da ganin an tabbatar da zaman lafiya a yankin, za ta nuna goyon baya ga“samar da kasashe biyu” da kuma mayar da Palasdinu a matsayin mamba a MDD. Amma ga abin da ‘yan siyasar Amurka suka yi, a zahiri dai, abin da ke jawo hankalinsu bai taba zama zaman lafiyar yankin gabas ta tsakiya ba, a maimakon hakan, abin da suke mai da hankali a kai shi ne kare muradunsu.

Labarai Masu Nasaba

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Amma abin farin ciniki shi ne, daukacin kasashen duniya na goyon bayan zaman lafiya da adalci. Don haka ma, muna da imanin cewa, ko ba dade ko ba jima, Palasdinu za ta samu kujerarta a MDD kamar yadda sauran mambobin MDD suke, kuma kasancewarsu kasashe biyu, Palasdinu da Isra’ila za su zauna lafiya da juna a tsakanin makwabciyar juna. (Mai zane: Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaDuniyaKasashen duniyaMajalisar Dinkin DuniyaMunafurciSinYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zuwa 2033 Bangaren Aikin Gona Na Kasar Sin Zai Samu Ci Gaba Ta Kowace Fuska

Next Post

Xi Ya San Burin Da Sin Take Son Cimmawa Da Kuma Makomarta

Related

Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

13 hours ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

7 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

1 week ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

2 weeks ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya San Burin Da Sin Take Son Cimmawa Da Kuma Makomarta

Xi Ya San Burin Da Sin Take Son Cimmawa Da Kuma Makomarta

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.