ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Amurka Ta Hau Kujerar Na Ki Ya Yayaye Lullubin Munafurcinta

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Amurka ta sake hana Palasdinawa cimma burinsu na kafa kasarsu mai ’yancin kai.

A ranar 18 ga wata, a yayin da kwamitin sulhun MDD ke kada kuri’u a kan wani daftarin shiri game da bukatar Palasdinu ta zama mamba a MDD, kasar Amurka ta sake hawan kujerar na ki, kuma ita ce kasa kadai da ta kada kuri’ar nuna rashin amincewa. Idan ba a manta ba, tuni a yau shekaru 13 da suka wuce, Palasdinu ta mika rokon zama mamba a MDD, amma sakamakon yadda ita Amurka ta hana, ba a kai ga mika shi ga babban taron MDD ba.

  • Kusan 90% Na Masu Amsa Tambayoyin Duniya Sun Yaba Da Gudummawar Da Sin Ke Bayarwa Ga Bunkasuwar Duniya Irin Na Kiyaye Muhalli, A Cewar Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN
  • Yankin Kudancin Tekun Pasifik Ba Zai Zamo Dandalin Hamayyar Kasashe Masu Karfi Ba, In Ji Ministan Wajen Sin

Sai dai ko shugaban kasar Amurka ko sauran manyan jami’an kasar, sau tari ne suka bayyana goyon bayansu ga shirin samar da kasashe biyu a matsayin hanya daya tilo mai dorewa ta zaman lafiya ta tsakanin Palasdinu da Isra’ila. To, amma idan ba ta amince da kafa kasar Palasdinu mai ’yancin kanta ba, ina ne za a yi zancen “samar da kasashe biyu”.

ADVERTISEMENT

Lallai amsa ita ce, zakin baki ba wani abu ba ne, amma kome shawara da za a yanke, dole ne ta amfana wa muradun kasar Amurka. Sanin kowa ne Amurka na da alaka ta kut da kut da Isra’ila ta fannoni daban daban, musamman ma a lokacin da Amurka ke dab da fara babban zaben kasar, ba za ta iya raba kai da Isra’ila ba. Idan Palasdinu ta kai ga zama mamba a MDD, za ta samu damar kara fito da muryarta a duniya tare da samun karin goyon baya, matakin da ka iya matsa wa Isra’ila, baya ga lalata muradun Amurka a yankin gabas ta tsakiya.

Rikici na ci gaba a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wanda yake ta haifar da mummunan tasiri ga sauran kasashen yankin. A cikin irin wannan hali, duk kasar da ke da niyyar tabbatar da ganin an tabbatar da zaman lafiya a yankin, za ta nuna goyon baya ga“samar da kasashe biyu” da kuma mayar da Palasdinu a matsayin mamba a MDD. Amma ga abin da ‘yan siyasar Amurka suka yi, a zahiri dai, abin da ke jawo hankalinsu bai taba zama zaman lafiyar yankin gabas ta tsakiya ba, a maimakon hakan, abin da suke mai da hankali a kai shi ne kare muradunsu.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Amma abin farin ciniki shi ne, daukacin kasashen duniya na goyon bayan zaman lafiya da adalci. Don haka ma, muna da imanin cewa, ko ba dade ko ba jima, Palasdinu za ta samu kujerarta a MDD kamar yadda sauran mambobin MDD suke, kuma kasancewarsu kasashe biyu, Palasdinu da Isra’ila za su zauna lafiya da juna a tsakanin makwabciyar juna. (Mai zane: Mustapha Bulama)

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Xi Ya San Burin Da Sin Take Son Cimmawa Da Kuma Makomarta

Xi Ya San Burin Da Sin Take Son Cimmawa Da Kuma Makomarta

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.