ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Amurka Ta Hau Kujerar Na Ki Ya Yayaye Lullubin Munafurcinta

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Amurka ta sake hana Palasdinawa cimma burinsu na kafa kasarsu mai ’yancin kai.

A ranar 18 ga wata, a yayin da kwamitin sulhun MDD ke kada kuri’u a kan wani daftarin shiri game da bukatar Palasdinu ta zama mamba a MDD, kasar Amurka ta sake hawan kujerar na ki, kuma ita ce kasa kadai da ta kada kuri’ar nuna rashin amincewa. Idan ba a manta ba, tuni a yau shekaru 13 da suka wuce, Palasdinu ta mika rokon zama mamba a MDD, amma sakamakon yadda ita Amurka ta hana, ba a kai ga mika shi ga babban taron MDD ba.

  • Kusan 90% Na Masu Amsa Tambayoyin Duniya Sun Yaba Da Gudummawar Da Sin Ke Bayarwa Ga Bunkasuwar Duniya Irin Na Kiyaye Muhalli, A Cewar Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN
  • Yankin Kudancin Tekun Pasifik Ba Zai Zamo Dandalin Hamayyar Kasashe Masu Karfi Ba, In Ji Ministan Wajen Sin

Sai dai ko shugaban kasar Amurka ko sauran manyan jami’an kasar, sau tari ne suka bayyana goyon bayansu ga shirin samar da kasashe biyu a matsayin hanya daya tilo mai dorewa ta zaman lafiya ta tsakanin Palasdinu da Isra’ila. To, amma idan ba ta amince da kafa kasar Palasdinu mai ’yancin kanta ba, ina ne za a yi zancen “samar da kasashe biyu”.

ADVERTISEMENT

Lallai amsa ita ce, zakin baki ba wani abu ba ne, amma kome shawara da za a yanke, dole ne ta amfana wa muradun kasar Amurka. Sanin kowa ne Amurka na da alaka ta kut da kut da Isra’ila ta fannoni daban daban, musamman ma a lokacin da Amurka ke dab da fara babban zaben kasar, ba za ta iya raba kai da Isra’ila ba. Idan Palasdinu ta kai ga zama mamba a MDD, za ta samu damar kara fito da muryarta a duniya tare da samun karin goyon baya, matakin da ka iya matsa wa Isra’ila, baya ga lalata muradun Amurka a yankin gabas ta tsakiya.

Rikici na ci gaba a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wanda yake ta haifar da mummunan tasiri ga sauran kasashen yankin. A cikin irin wannan hali, duk kasar da ke da niyyar tabbatar da ganin an tabbatar da zaman lafiya a yankin, za ta nuna goyon baya ga“samar da kasashe biyu” da kuma mayar da Palasdinu a matsayin mamba a MDD. Amma ga abin da ‘yan siyasar Amurka suka yi, a zahiri dai, abin da ke jawo hankalinsu bai taba zama zaman lafiyar yankin gabas ta tsakiya ba, a maimakon hakan, abin da suke mai da hankali a kai shi ne kare muradunsu.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Amma abin farin ciniki shi ne, daukacin kasashen duniya na goyon bayan zaman lafiya da adalci. Don haka ma, muna da imanin cewa, ko ba dade ko ba jima, Palasdinu za ta samu kujerarta a MDD kamar yadda sauran mambobin MDD suke, kuma kasancewarsu kasashe biyu, Palasdinu da Isra’ila za su zauna lafiya da juna a tsakanin makwabciyar juna. (Mai zane: Mustapha Bulama)

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Xi Ya San Burin Da Sin Take Son Cimmawa Da Kuma Makomarta

Xi Ya San Burin Da Sin Take Son Cimmawa Da Kuma Makomarta

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.