• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bikin Ranar Hausa Ya Gudana A Nijeriya Da Wasu Kasashen Duniya

by Mustapha Ibrahim
3 years ago
in Rahotonni
0
Yadda Bikin Ranar Hausa Ya Gudana A Nijeriya Da Wasu Kasashen Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An dai ware ranar 26 ga watan Agusta na kowacce shekara ta kasance ranar bikin Hausa ta duniya, rana ce da ta samo asali tun a shekarar 1910 daga wani Bature wanda ya kirkiri harafin K,D,B,da kalmar KWA, KYA da sauransu.

An sake habaka bikin a ‘yan shekarun nan ta hanyar tunawa da ranar a shafukan sada zumunta.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Sojoji Kwanton Bauna, Sun Kashe Sojoji 2 A Katsina
  • Ma’aikatan Gwamnati Sun Fi ‘Yan Siyasa Cin Hanci Da Rashawa – Kwamitin Majalisar Dattawa

Bayanai sun tabbatar da cewa an fara gudanar da wannan biki tun shekaru 100 da suka gabata, inda a yanzu ake gudanarwa a duk fadin duniya wanda yake nuna cewa, Hausa harshe ne mai albarka da karbuwa a duniya kamar dai yadda bikin ke nunuwa.

A Kano, Kungiyar Marubuta ta shirya bikin ranar ne a Makarantar Nazarin Harshen Larbci da Shari’a ta Malam Aminu Kano a ranar Juma’ar da ta gabata da kuma wasu ranaku, saboda bunkasa wannan rana.

Da yake jawabi a wurin bikin, Sarkin Hausawan Afirka kuma Sardauna Agadaz, Dakta Abdulkadir Labaran Koguna ya bayyana cewa albarkar harshen Hausa ya sa babu wani harshe da yake da haruffa a Nijeriya ko ma a wasu kasashen da za a iya rubuta alkur’ani mai girma cikin sauki kamar sa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Ya ce sauran harsuna kamar Yoruba, Ibo, Fulatanci da makamantansu suna da wuya wajen rubuta alkur’ani mai girma da su, domin a Hausa ne ake da alu, anbaki, alikafa irin na Larabci kuma ko ma wajen rera karatun kur’ani in aka saurari Yarabawa za ka ga ya sha bamban, saboda ba su da harufa kamar yadda Hausa take da su.

Rahotanni sun bayyana cewa an gudanar da bukukuwan ranar Hausa ta duniya a dukkan jihohin Nijeriya guda 36 ciki har da Abuja.

A Jihar Kano, an gudanar da bikin a fadar Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, inda aka gwangwaje da bayanan ranar Hausa da kuma karbar bakuncin kungiyoyi masu alaka da Hausa daga jihohin Gombe, Zamfara wadanda suka halarci taron na fadar Sarkin Kano a ranar Juma’ar da ta gabata.

Haka ma a fadar Mai Martaba Sarkin Dutse, Alhaji Nuhu Muhammadu Sanusi, da ke Jihar Jigawa an yi kasaitaccen biki, inda aka fadada Daular Sarkin Hausawan Afirka ta hanyar nada sarautu 7 na sarkin Hausawa a Nijeriya, wanda aka nada Alhaji Munir na Kura a matsayin Galadiman Sarkin Hausawa na Jamhuriyar Benin, sai sarkin Hausawan Sudan da aka nada Alhaji Shamsudeen da sarkin wakar Hausawan Afirka, Alhaji Sani Kaka Dawa, da dai sauran masarautu ga masu kishin harshen Hausa da kuma al’adunsu.

Hakazalika, an gudanar da bikin na ranar Hausa a kasashe 49 cikin kasashe 59 na Nahiyar Afrika da ake da su da wasu kasashe da ke kan tsuburi.

Haka kuma bikin ya gudana a manyan kasashe irin su Saudiyya, China, Amurka, Faransa, da sauran su.

A dai cikin jawabin Sarkin Hausawan Afirka, Dakta Abdulkadir Labaran Koguna ya ce “Daukakar Hausa a duniyarmu ta yau ya sa a 2019, Hausa ta zama harshe na 13 a duniya, amma yanzu za ka samu Hausa a mataki na 9 ko na 8 a duniya.

“Yanzu Hausa ita ce harshen na 4 da ake fadakar da mutane da shi a wajen jifan Shedan a wurin a aikin Hajji a kasar Saudiyya.

A shekaru 3 da suka wuce kuma Hausa ce harshe na 7 cikin harsuna 9 da ake fassara huduba a Masallacin Harami a aikin Hajji a shekarun da suka gabata.

Harshen Hausa ya samu daukaka da dama a duniya.” Har ila yau, Dakta Koguna ya warware zare da abawa a kan munakisar da ake kokarin kitsawa don haddasa sabuwar gaba a tsakanin Hausawa da Fulani dangane da Jihadin Shehu Usman Danfodiyo.

“Kishin Hausa muke yi ba maguzancin da Shehu Usman Danfodiyo ya yaka ba, wani sabon makirci da muka lura ya bullo shi ne, cusa kiyayyar Fulani a zukatan Hausawa da kuma cusa kiyayyar Hausawa ga Fulani, musamman tarihin karyar da ake yadawa na cewa Shehu Usman Danfodiyo ya yaki Hausawa, sannan ya kafa Daular Fulani.

Wannan makirci ne babba a lura da shi tare da yin hattara, saboda ana amfani da ‘yan daban Hausa wajen afka wa Fulani sakamakon wannan makirci.

Haka kuma ana amfani da ‘yan daban Fulani wajen afka wa Hausawa tare da aibata Danfodiyo wai ya kau da al’adun Hausawa na tarihi.

“Danfodiyo al’adun maguzanci ya kawar ya kawo na musulunci, kuma musulunci ne gaba da Hausa da Fulantaci, aibata Danfodiyo maguzanci ne kuma makirci ne daga makiyanmu na nesa da na kusa, ya kamata a yi hattara da irin wadannan abubuwa.”

Shi ma Sarkin Hausawan Tukulmawa da ke Jihar Gombe, Alhaji Ibrahim Haruna, wanda har ila yau shi ne shugaban Kungiyar Arewanmu Duniyarmu da ta hada harsuna da kabilun arewa kaf, mai shalkwata a Kaduna, ya tofa albarkacin bakinsa a lokacin kungiyoyi suka gabatar da jawabai a ranar Hausar a fadar Mai Martaba Sarkin Kano.

Tukulmawa ya ce kungiyarsu ta hada kan kabilun arewa, wanda Hausawa ne kan gaba kuma aikinta shi ne fahimtar juna da samar da hadin kai, tsaro, yakar zalunci ba tare da la’akari da addini ko harshe ba.

A cewarsa, akwai wani sashi na shugabanci a wannan kungiya wanda ya kunshi Malaman Musulunci da na Kirista domin cimma burinmu na ceton arewa da Nijeriya baki daya.

Ya kara da cewa a cikin malaman Musulunci na wannan kungiyar akwai Sheik Adam Mai Hula, Sheik Sambo Rigacikum, sai kuma Fasto Yohana Buru, Rabaran Abarakallah, shugaban CAN na arewa.

Shi kuwa Gafakan Gombe, Alhaji Musa Ahmad Muhammad ya yi kira ne a yi amfani da ranar Hausa ta duniya wajen yi wa Nijeriya addu’a ta samun tsaro da zaman lafiya.

Ita kuwa shugabar mata da matasa daga jihar Zamfara, Hajiya Fatima ta ce su mata za su dage wajen raya al’adun Hausawa ta hanyar saka sutura a ko ina fadin duniya.

Dakta Hassan Sulaiman Kofar Naisa, masani kuma tsohon ma’aikacin fadar shugaban kasa da ya yi ritaya, ya ce Hausawa na sahun gaba wajen kyawawan al’adu da dabi’u masu kyau a duniya.

“Mu Hausawa muna da zumunci, kunya, kara, saukin kai, tawali’u, rikon alkawari, sanin ya kamata da sauran su. Duk Bahaushen asali yana alfahari da wadannan al’adu da muka gada tun lokacin kaka da kakanin.

“Abin da ya sa na tabbatar da haka shi ne, na yi yawo a wannan duniya daidai bakin gwargwado ta dalilin aiki ko na neman ilimi. Abin da ya fi ba ni shi sha’awa da mamaki na al’adar Hausawa shi ne, sai da na girma na gane matar mahaifina da ke tare da mahaifiyata ba ita ce ta haife ni ba, saboda ita ce take yi min komai, domin a gurinta nake.

“Haka shi ma dan’uwana ya samu kansa, ba za ka taba samun wannan dabi’a mai kyau ba in ba a cikin Hausawa ba. Bahaushe ya yi sa’a da ya kamata ya rike al’adarsa da alfaharin a fadin duniya, kuma har yanzu ba mu san abin da ake cewa mace ta yi yaji a gidanmu ba.”

A bana dai bikin rana rya fi mayar da hankali ne a kan yadda za a tabbatar da zaman lafiya da kaunar juna a tsakanin al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BahausheHarsheHausawaKadunakanoNijarNijeriyaRanar HausaYare
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Za Ta Binciki Musabbabin Rushewar Benen Titin Beirut -Ganduje

Next Post

Abin Da Ya Sa Mata Suka Fi Fuskantar Yiwuwar Kashe Kansu —Farfesa Aishatu

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Abin Da Ya Sa Mata Suka Fi Fuskantar Yiwuwar Kashe Kansu —Farfesa Aishatu

Abin Da Ya Sa Mata Suka Fi Fuskantar Yiwuwar Kashe Kansu —Farfesa Aishatu

LABARAI MASU NASABA

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.