• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba

by yahuzajere
1 year ago
in Rahotonni
0
Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya kaddamar da rabon abinci kyauta ga al’ummar Musulmi akalla 10,000 a Jihar Kano, jiharsa ta asali, ta hannun Gidauniyar Aliko Dangote.

Har ila yau, gidauniyar ta fadada karamcin ta hanyar raba buhunan shinkafa miliyan daya da kudinsu ya haura Naira biliyan 13 a fadin jihohi 36 na tarayya da Babban Birnin Tarayya Abuja domin rage yunwa a kasar nan.

Manufar wannan tallafi ita ce a sassauta wa miliyoyin ‘yan Nijeriya matsin da suke sha sakamakon kalubalen tattalin arziki da kasar ke fama da shi.

Wannan duka kari ne a kan rabon burodi 20,000 a kullum ga mazauna Kano da kuma wasu 15,000 ga mazauna Legas, inda tsarin ciyarwar da aka fara kuma ya dore tun daga 2020 a lokacin annobar COVID-19.

Abincin da ake dafawa na buda-bakin Ramadan kyauta ya hada da shinkafa dafa-duka, farar shinkafa da miya, taliya dafa-duka, doya, wake da naman kaza da na saniya, kana da ruwan sha na gora ga kowane mutum.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

  • ‘Yan Ta’adda Sun Sake Sace Mutane 87 A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Kaduna

Ana raba kunshin abincin ne a masallatan Juma’a da tituna da gidajen yari da gidajen marayu da gidajen riman (na tsare mutane) da sauran wurare a cikin birnin Kano da kewaye.

Wani da ya ci gajiyar abincin mai suna Musa Maikatako, mazaunin Tarauni ya nuna jin dadinsa da wannan karimcin wanda ya ce ya taimaka masa wajen yin buda baki cikin sauki.

Maikatako, wanda a bayyane fuskarsa na cike da farin ciki, ya ce abinci na kyauta ya kawar da wahalhalun da jama’a da dama za su iya fusktan wajen yin buda baki da ruwa kawai, ba tare da abinci ba, bisa la’akari da halin kuncin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

“Ba zan iya bayyana irin farin cikin da nake ciki ba, wannan abincin zai taimaka matuka wajen taimaka wa talakawa kamar ni mu samu abin da za mu yi buda baki da abinci mai nauyi.

“Na san mutane da yawa a jihar nan wadanda za su iya yin buda baki da ruwa kawai. Don haka wannan abincin ya kawo sauki kwarai da gaske,” in ji shi.

Da yake nuna farin cikinsa, Maikatako ya nuna godiya ga Gidauniyar Dangote bisa wannan karamcin, inda ya yi addu’ar Allah ya kara masa arziki, ya kuma ci gaba da sanya albarka a kasuwancinsa.

Har ila yau, wata da ta ci gajiyar tallafin, Hajiya Inna Tukur, ta bayyana jin dadin ta da rabon abincin, wanda a cewarta Gidauniyar Aliko Dangote ta kawo mata dauki.

A cewar Inna, ta yi farin ciki da irin wannan abinci mai dadi da ake ba ta kyauta a halin matsin da ake ciki.

“A cikin wahalhalun da ake fama wanda yana da kamar wuya mu iya cin abinci ko da sau biyu a rana, amma sai ga shi cikin ludufi, an samu wani yana taimaka mana da abinci mai lagwada, gaskiya wannan ba karamin abu ba ne.

“Ba abin da zan ce sai dai in yi godiya ga ku da Aliko Dangote, ina rokon Allah ya kara muku albarka.”

Baya ga rabon burodi da aka kwashi tsawon shekara 4 ana yi kyauta, Gidauniyar Dangote ta shafe sama da shekaru 30 tana ciyar da mabukata a Kano. Ana yin hakan ne daga gidan mahaifiyarsa da ke Koki da kuma wasu wuraren dafa abinci daban-daban. Wannan shiri na ciyarwa yana ciyar da mazauna Kano 10,000 a kullum tun daga karin kumallo, abincin rana, da kuma abincin dare tsawon shekara 30 ba fashi.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciDangotekanoMabukataRaboRamadanTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Wasu Ka’idojin Kula Da Muhalli Dake Mayar Da Hankali Kan Yankuna Daban-daban

Next Post

Bayan Kwance Alakar Soji Da Faransa, Nijar Ta Sake Raba Gari Da Sojin Amurka 

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
dangote
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Bayan Kwance Alakar Soji Da Faransa, Nijar Ta Sake Raba Gari Da Sojin Amurka 

Bayan Kwance Alakar Soji Da Faransa, Nijar Ta Sake Raba Gari Da Sojin Amurka 

LABARAI MASU NASABA

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.