• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba

by yahuzajere
1 year ago
in Rahotonni
0
Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya kaddamar da rabon abinci kyauta ga al’ummar Musulmi akalla 10,000 a Jihar Kano, jiharsa ta asali, ta hannun Gidauniyar Aliko Dangote.

Har ila yau, gidauniyar ta fadada karamcin ta hanyar raba buhunan shinkafa miliyan daya da kudinsu ya haura Naira biliyan 13 a fadin jihohi 36 na tarayya da Babban Birnin Tarayya Abuja domin rage yunwa a kasar nan.

Manufar wannan tallafi ita ce a sassauta wa miliyoyin ‘yan Nijeriya matsin da suke sha sakamakon kalubalen tattalin arziki da kasar ke fama da shi.

Wannan duka kari ne a kan rabon burodi 20,000 a kullum ga mazauna Kano da kuma wasu 15,000 ga mazauna Legas, inda tsarin ciyarwar da aka fara kuma ya dore tun daga 2020 a lokacin annobar COVID-19.

Abincin da ake dafawa na buda-bakin Ramadan kyauta ya hada da shinkafa dafa-duka, farar shinkafa da miya, taliya dafa-duka, doya, wake da naman kaza da na saniya, kana da ruwan sha na gora ga kowane mutum.

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

  • ‘Yan Ta’adda Sun Sake Sace Mutane 87 A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Kaduna

Ana raba kunshin abincin ne a masallatan Juma’a da tituna da gidajen yari da gidajen marayu da gidajen riman (na tsare mutane) da sauran wurare a cikin birnin Kano da kewaye.

Wani da ya ci gajiyar abincin mai suna Musa Maikatako, mazaunin Tarauni ya nuna jin dadinsa da wannan karimcin wanda ya ce ya taimaka masa wajen yin buda baki cikin sauki.

Maikatako, wanda a bayyane fuskarsa na cike da farin ciki, ya ce abinci na kyauta ya kawar da wahalhalun da jama’a da dama za su iya fusktan wajen yin buda baki da ruwa kawai, ba tare da abinci ba, bisa la’akari da halin kuncin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

“Ba zan iya bayyana irin farin cikin da nake ciki ba, wannan abincin zai taimaka matuka wajen taimaka wa talakawa kamar ni mu samu abin da za mu yi buda baki da abinci mai nauyi.

“Na san mutane da yawa a jihar nan wadanda za su iya yin buda baki da ruwa kawai. Don haka wannan abincin ya kawo sauki kwarai da gaske,” in ji shi.

Da yake nuna farin cikinsa, Maikatako ya nuna godiya ga Gidauniyar Dangote bisa wannan karamcin, inda ya yi addu’ar Allah ya kara masa arziki, ya kuma ci gaba da sanya albarka a kasuwancinsa.

Har ila yau, wata da ta ci gajiyar tallafin, Hajiya Inna Tukur, ta bayyana jin dadin ta da rabon abincin, wanda a cewarta Gidauniyar Aliko Dangote ta kawo mata dauki.

A cewar Inna, ta yi farin ciki da irin wannan abinci mai dadi da ake ba ta kyauta a halin matsin da ake ciki.

“A cikin wahalhalun da ake fama wanda yana da kamar wuya mu iya cin abinci ko da sau biyu a rana, amma sai ga shi cikin ludufi, an samu wani yana taimaka mana da abinci mai lagwada, gaskiya wannan ba karamin abu ba ne.

“Ba abin da zan ce sai dai in yi godiya ga ku da Aliko Dangote, ina rokon Allah ya kara muku albarka.”

Baya ga rabon burodi da aka kwashi tsawon shekara 4 ana yi kyauta, Gidauniyar Dangote ta shafe sama da shekaru 30 tana ciyar da mabukata a Kano. Ana yin hakan ne daga gidan mahaifiyarsa da ke Koki da kuma wasu wuraren dafa abinci daban-daban. Wannan shiri na ciyarwa yana ciyar da mazauna Kano 10,000 a kullum tun daga karin kumallo, abincin rana, da kuma abincin dare tsawon shekara 30 ba fashi.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciDangotekanoMabukataRaboRamadanTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Wasu Ka’idojin Kula Da Muhalli Dake Mayar Da Hankali Kan Yankuna Daban-daban

Next Post

Bayan Kwance Alakar Soji Da Faransa, Nijar Ta Sake Raba Gari Da Sojin Amurka 

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 day ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

7 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

7 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
Bayan Kwance Alakar Soji Da Faransa, Nijar Ta Sake Raba Gari Da Sojin Amurka 

Bayan Kwance Alakar Soji Da Faransa, Nijar Ta Sake Raba Gari Da Sojin Amurka 

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.