• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke Daura a Jihar Katsina ya zama fadar ziyarar manyan ‘yan siyasar Nijeriya.

A wannan makon dai, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa a karkashin tutar jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya ziyarci Buhari a gidansa da ke Daura a Jihar Katsina, inda suka yi ganawar sirri tare da tsohon wamnan Jihar Sakkwato kuma sanata mai wakiltar Sakkwato ta kudu, Aminu Waziri Tambuwal.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya

Sai dai ba a samu cikakken bayani kan tattaunawar da fitattun ‘yan siyasar suka yi ba, amma wasu manazarta na ganin ziyarar a matsayin wata dabarar da Atiku ya dauka na tabbatar da samun nasara a zaben shugaban kasa a 2027.

Amma a wata sanarwa da ya fitar, mai bai wa Atiku shawara kan harkokin yada labarai, Mista Paul Ibe ya ce tsohon mataimakin shugaban kasar ya kai ziyarar jaje ne Jihar Katsina.

Sanarwar ta ce, “Tsohon mataimakin shugaban kasar Nijeriya kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben shugaban a 2023, Atiku Abubakar ya jagoranci sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar zuwa gidan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Alhaji Lawan Kaita a Daura wajen kai gaisuwar ta’aziyyar mutuwa da aka yi wa iyalan.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

“Ziyarar wacce ta samu kyakkyawar tarba ga Atiku a manyan garuruwan masarautar Daura, sannan tsohon mataimakin shugaban kasar ya kai irin wannan ziyarar ga Sarkin Daura, Alhaji Farouk Umar Farouk da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

“Taron da Atiku Abubakar ya yi a Jihar Katsina, ci gaba ne da ziyarar ban girma da ya kai tun bayan kammala bukukuwan Sallah da kuma jajanta wa iyalan tsohon abokinsa, Malam Lawan Kaita,” in ji shi.

Sanarwarta kara da cewa Atiku ya kuma ziyarci Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman.

Kwanaki biyar kafin tafiyar tasa zuwa Daura, tsohon mataimakin shugaban kasa ya kai ziyara daban-daban ga tsaffin shugabannin sojoji, Ibrahim Badamasi Babangida da Abdulsalami Abubakar a gidajensu Minna a babban birnin Jihar Neja.

Wannan ita ce ziyara ta farko da Atiku ya yi wa Buhari tun bayan da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zabukan 2019 da 2023 ya fice daga jam’iyyar APC.

An kuma bayyana ziyarar tsohon shugaban kasan a matsayin wani dabarar siyasa da Atiku ya dauka”, musamman a daidai lokacin da yake kokarin hadakar jam’iyyun adawa don kwace mulki a wurin jam’iyyar APC karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu a 2027.

Yunkurin nasa ya kara daukar hankali a watan da ya gabata lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben bara, Peter Obi, ya kai masa ziyarar ban girma. Obi shi ne abokin takarar Atiku a zaben shugaban kasa na 2019 da suka fafata da Buhari. Bayan sa’o’i 24 da ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari, shi ma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru el-Rufai ya kai irin wannan ziyarar ga tsohon shugaban kasa a gidansa da ke Daura.

Kafin yanzu, gidajen tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo da tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Ibrahim Babangida da tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar, ya kasance wurin da ‘yan siyasa ke tururun kai ziyara.

Sai dai gidan tsohon shugaban kasa Buhari da ke Daura na ci gaba da ganin shahararrun ‘yan siyasa, musamman daga yankin arewacin Nijeriya.

Haka kuma, shi ma tsohon gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff yana daga cikin manyan ‘yan siyasan da suka kai wa tsohon shugaban kasa Buhari ziyara a gidansa da ke Daura.

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya soki wannan ziyarar da ‘yan siyasar arewa suke kai wa tsohon shugaban kasa Buhari. Yana mai cewa wannan wani yunkuri ne da ‘yan siyasan arewa suke yi na shirin tunkude shugaban kasa, Bola Tinubu a 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SiyasaBuhariZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Bukatar Mu Bai Wa Mara Ɗa Kunya A Gasar EURO Ta Bana – Gordon

Next Post

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Buhari
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

2 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

2 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

2 weeks ago
Next Post
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.