• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke Daura a Jihar Katsina ya zama fadar ziyarar manyan ‘yan siyasar Nijeriya.

A wannan makon dai, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa a karkashin tutar jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya ziyarci Buhari a gidansa da ke Daura a Jihar Katsina, inda suka yi ganawar sirri tare da tsohon wamnan Jihar Sakkwato kuma sanata mai wakiltar Sakkwato ta kudu, Aminu Waziri Tambuwal.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya

Sai dai ba a samu cikakken bayani kan tattaunawar da fitattun ‘yan siyasar suka yi ba, amma wasu manazarta na ganin ziyarar a matsayin wata dabarar da Atiku ya dauka na tabbatar da samun nasara a zaben shugaban kasa a 2027.

Amma a wata sanarwa da ya fitar, mai bai wa Atiku shawara kan harkokin yada labarai, Mista Paul Ibe ya ce tsohon mataimakin shugaban kasar ya kai ziyarar jaje ne Jihar Katsina.

Sanarwar ta ce, “Tsohon mataimakin shugaban kasar Nijeriya kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben shugaban a 2023, Atiku Abubakar ya jagoranci sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar zuwa gidan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Alhaji Lawan Kaita a Daura wajen kai gaisuwar ta’aziyyar mutuwa da aka yi wa iyalan.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

“Ziyarar wacce ta samu kyakkyawar tarba ga Atiku a manyan garuruwan masarautar Daura, sannan tsohon mataimakin shugaban kasar ya kai irin wannan ziyarar ga Sarkin Daura, Alhaji Farouk Umar Farouk da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

“Taron da Atiku Abubakar ya yi a Jihar Katsina, ci gaba ne da ziyarar ban girma da ya kai tun bayan kammala bukukuwan Sallah da kuma jajanta wa iyalan tsohon abokinsa, Malam Lawan Kaita,” in ji shi.

Sanarwarta kara da cewa Atiku ya kuma ziyarci Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman.

Kwanaki biyar kafin tafiyar tasa zuwa Daura, tsohon mataimakin shugaban kasa ya kai ziyara daban-daban ga tsaffin shugabannin sojoji, Ibrahim Badamasi Babangida da Abdulsalami Abubakar a gidajensu Minna a babban birnin Jihar Neja.

Wannan ita ce ziyara ta farko da Atiku ya yi wa Buhari tun bayan da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zabukan 2019 da 2023 ya fice daga jam’iyyar APC.

An kuma bayyana ziyarar tsohon shugaban kasan a matsayin wani dabarar siyasa da Atiku ya dauka”, musamman a daidai lokacin da yake kokarin hadakar jam’iyyun adawa don kwace mulki a wurin jam’iyyar APC karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu a 2027.

Yunkurin nasa ya kara daukar hankali a watan da ya gabata lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben bara, Peter Obi, ya kai masa ziyarar ban girma. Obi shi ne abokin takarar Atiku a zaben shugaban kasa na 2019 da suka fafata da Buhari. Bayan sa’o’i 24 da ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari, shi ma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru el-Rufai ya kai irin wannan ziyarar ga tsohon shugaban kasa a gidansa da ke Daura.

Kafin yanzu, gidajen tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo da tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Ibrahim Babangida da tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar, ya kasance wurin da ‘yan siyasa ke tururun kai ziyara.

Sai dai gidan tsohon shugaban kasa Buhari da ke Daura na ci gaba da ganin shahararrun ‘yan siyasa, musamman daga yankin arewacin Nijeriya.

Haka kuma, shi ma tsohon gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff yana daga cikin manyan ‘yan siyasan da suka kai wa tsohon shugaban kasa Buhari ziyara a gidansa da ke Daura.

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya soki wannan ziyarar da ‘yan siyasar arewa suke kai wa tsohon shugaban kasa Buhari. Yana mai cewa wannan wani yunkuri ne da ‘yan siyasan arewa suke yi na shirin tunkude shugaban kasa, Bola Tinubu a 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SiyasaBuhariZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Bukatar Mu Bai Wa Mara Ɗa Kunya A Gasar EURO Ta Bana – Gordon

Next Post

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.