• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto

by Sadiq
3 years ago
in Rahotonni
0
Yadda Hare-Haren ‘Yan Bindiga Suka Shafi Rayuwar Al’umma A Kagara – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoto da kafar yada labarai ta PRNigeria ta fitar ya nuna cewa hare-haren da ake kai wa al’ummar Chonoko a jihar Kebbi, da kuma al’ummar Kagara a jihar Neja sun taimaka matuka gaya wajen raguwar kwararrun likitocin kiwon lafiya, da ayyukan ilimi, da sauran ayyukan jin kai a jihohin.

Baya ga kalubalen rashin tsaro da ake fama da shi, rahoton ya yi nuni da cewa, rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijirar ta zama abu mai wahala, ganin yadda jama’a ke matukar bukatar manyan ababen more rayuwa na dan Adam kamar abinci, ruwa, matsuguni da dai sauransu. .

  • Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane
  • Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

Sai dai kafar yada labaran ta zargi masu ruwa da tsaki a jihar da yin sama da fadi da kayan agajin da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayar ga al’ummomin da ba su da karfi.

Wakilin PRNigeria, Mukhtar Madobi ne, ya bayyana hakan a yayin wani taron bita na yini biyu a Abuja mai taken: ‘Yan Jarida na Jin kai don Ci gaban Tattalin Arziki’ a lokacin da yake gabatar da wani bincike kan halin jin kai da kuma halin da ‘yan gudun hijira ke ciki a jihohin Kebbi da Neja.

Ya yi nuni da cewa ilimi wani bangare ne mai matukar muhimmanci wanda shi ma yake fama da matsalar rashin tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Sakamakon binciken ya nuna cewa an rufe akasarin makarantu a kauyukan saboda fargabar hare-haren ‘yan bindiga.

“Manoma a wasu kauyukan da ke kusa da su sun koma biyan haraji ga ‘yan bindiga domin samun damar shiga gonakinsu da gudanar da ayyukan noma. Duk da haka, ayyukan noma sun ragu sosai ta yadda hakan ya haifar da karuwar matsalar karancin abinci.

“Yawancin makarantun kauyukan a rufe suke saboda fargabar hare-haren ‘yan bindiga, wanda hakan ya shafi fannin ilimi a yankin.”

Rahoton ya kara da cewa, “Yanzu haka harkar kiwon lafiya an mata kisan mummuke, saboda Babban Asibitin garin ba ya aiki yadda ya kamata saboda fargabar ‘yan bindiga.”

A halin da ake ciki, wasu asibitocin da ke cikin garuruwan an mayar da su sansanonin ‘yan gudun hijira inda ake kula da wadanda abin ya shafa.

Ya koka da yadda lamarin ya sa dalibai da dama daina zuwa makarantu, wanda hakan ya kara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yankin da ma kasar baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiHare-HareKagaraKebbiMakarantuNejaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Kasuwannin Da Aka Fi Samun Goruba A Nijeriya

Next Post

Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

1 week ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

2 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

2 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.