• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mata Ke Daukar Yara Don Taya Su Aikin Gida

by Leadership Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Taskira
0
Maganin Zubewar Mama Da Yadda Ake Gyara Shi 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau canjin yanayin wannan zamanin ya zo wa da mata wani sabon salo da yadda suke daukan ‘yara domin taya su aiki a gida.

Wasu su kan sakar wa mai aiki ragamar aikin gida, har ya kai ga basu koya wa ‘ya’yansu mata girki domin wasu ana yin aurensu basu iya girki ba. Ko me za ku ce akan hakan? Shafin Taskira shafi ne da ya saba zakolo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma. Tsokacimmu na yau zai yi doba ne game da yadda ake samu, ana auran yara mata basu iya Girki ba:

 

Usman Sani

Gaskiya wannan batu yana da muhimmanci sosai. Yanzu zamanin ya canza, kuma yawancin iyaye suna daukar ma’aikata don su taimaka a ayyukan gida. Wannan ba matsala bace idan dai iyayen suna koyar da ’ya’yansu abubuwan da suka kamata, musamman girki.

Labarai Masu Nasaba

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

Amma idan aka bar wa mai’aikata duk aikin gida, kuma iyaye ba su ba wa ’ya’yan nasu lokaci don koya musu girki ba, lamarin zai iya zama matsala. A lokacin aure, wasu matan za su fuskanci kalubale saboda ba su da gogewa.

Ina ganin wajibi ne iyaye su rika koya wa ’ya’yansu mata abubuwan da suka dace, ko da kuwa akwai ma’aikata a gida. Wannan zai taimaka musu su zama masu cikakkiyar basira da iya kula da gida a gaba. Wannan kuma ba zai hana daukar ma’aikata ba, amma ba dole a jingina komai a kansu ba.

 

Khadija Abdullahi

To gaskiya rashin iya girki ga mace ba karamar matsala bace, saboda bai kamata ace tunda aka haifeki har kika taso koka girma ace baki iya girki ba wannan gaskiya abun kunya ne.

Ya kamata ace iyaye su dage, suyi iya kokarinsu danganin sun koyawa yaransu girki, tun yarinya na karama yakamata afara koyamata ahankali ahankali hatta girma, kafin yarinya ta girma sai ki ga ta iya aikinta. Amma da zarar annuna wa yarinya so an bar ta ba a koya mata komai ba haka za ta girma ba ta iya komai ba, kuma ta zo ta wahala daga baya tun da dole sai ta yi, ba za a tattaba ta yi aure ba, sannan ba ka san wanda za ta aura ba ya yanayin halinsa yake, wani komai halinsa ba ya son mai aiki ya fi son matarsa ta yi masa girki da kanta.

Shawara ga iyaye mata mu cire son ‘ya’yanmu, mu koya musu girki kala-kala, duk inda za su shiga ba za su ji kunya ba saboda sun san sun iya komai, amma idan basu iya ba sai ki ga su kansu suna jin kunyar shiga mutane. Ki koya wa ‘ya’yanki aiki wannan shi ne gata. Allah ya sa mu dace.

 

Fa’iza Musa

To ni a ganina gaskiya ka koyawa ‘ya’yanka mata aikin gida shi ne gata, ba wai ka bar su sakaka ba komai a ce mai aiki ce za ta yi gaskiya wannan ba daidai ba ne, ba kuma so bane, ni ina ganin ma cutarsu kake. Ya kamata iyaye su koyawa ‘ya’yansu aikin gida ba wai girki kadai ba komai na gida yadda kyau yarinya mace ta iya kome na gida.

Sakarwa mai aiki ragamar gida ba kya koyawa ‘ya’yanki aiki ba wannan gaskiya ba karamin cutar kai bane.

Wai sai ki ga sai za a yi auren yarinya sannan ne za a kai ta wajen koyon girki a biya kudi mai yawa, wai a wannan lokacin ne za ta koyi duk wani girki, ai wannan lokacin ya yi kankanta, sannan kuma ko ta ko ya iyakarta ta yi na doki, ba za ta iya dorewa ba daga baya ta watsar tun da ba ta saba ba, ba lallai ne ta iya dorewa ba, a zo kuma a shiga wani yanayi. Allah ya ganar da mu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kirsimeti: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 15 Da Ake Zargi Da Laifin Sata A Bauchi

Next Post

Bitar Aikin Hajjin 2024

Related

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?
Taskira

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

1 month ago
Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa
Taskira

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

2 months ago
Mata
Taskira

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

2 months ago
Matsalolin Da Ke Tattare Da Zawarci Da Rashin Yin Aure Da Wuri
Taskira

Matsalolin Da Ke Tattare Da Zawarci Da Rashin Yin Aure Da Wuri

3 months ago
‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
Taskira

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

6 months ago
Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
Taskira

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

7 months ago
Next Post
Mata

Bitar Aikin Hajjin 2024

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.