ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bitar Aikin Hajjin 2024

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Hajjin 2024

Aikin Hajjin 2024, ya ajiye tarihin da ba za a manta da shi ba a tarihin aikin hajjin da Nijeriya ta halarta a kasar Saudiyya ta fuskoki da dama sakamakon tsare-tsaren da Hukumar jin dadin alhazai ta kasa, NAHCON ta aiwatar.

 

NAHCON, a karkashin jagorancin Malam Jalal Ahmad Arabi ta samu nasarori da yabo daga mahajjata da masu sanya ido a harkokin aikin hajji bisa aiwatar da tsare-tsaren kwarewa da hukumar ke da shi a tarihinta. Sai dai ana cewa, Ubangiji ne kadai ya cika 100 bisa 100.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Lalata Matatun Mai 20 A Yankin Niger Delta
  • Yadda Mai Haihuwar Fari Za Ta Kula Da Kanta (2)

Kwararren masanin aikin Hajji, Ustaz Abubakar Siddeq Muhammad, a cikin sharhinsa mai suna “Mal. Jalal Ahmad Arabi a aikin Hajjin 2024 (2)” wanda Kamfanin jaridar LEADERSHIP ya buga, ya yaba da tsare-tsaren shirye-shiryen Arafah da ba a taba yin irinsa ba inda ya ce. “A karon farko cikin fiye da shekaru 20, an shirya tantunan Nijeriya tsaf, an baje shimfidar kafet da na’urorin sanyi,” in ji shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Tuggar Ya Sabunta Harkokin Diflomasiyyar Nijeriya

Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON

Bugu da kari, wani masanin ayyukan aikin hajji, ya yi sharhi da tsokaci game da nasarorin da Arabi ya samu a lokacin jagorancinsa a matsayin shugaban hukumar NAHCON, kamar yadda aka buga a: “https://www.hajjnews.com.ng/2024/12/nahcon-in-2024-year-of-achievements-challenges-and-renewal.html”

 

Duk da cewa, rayuwa ba matabbata ba ce, haka ma, mulki ko jagoranci, suna da lokaci da iyaka. An yanke wa’adinsa jagorancinsa saboda wasu dalilai na siyasa da zarge-zarge amma shugabancin Jalal Arabi a matsayin Shugaban Hukumar NAHCON ya ba da sakamako wanda ya kawo sauyi, wanda a halin yanzu ke tabbace cikin cikakken bayanin rahoton Hukumar na 2024, mai taken “2024: Shekarar Nasarori, Kalubale, da Sabuntawa”.

 

Shugaban kasa, Bola Tinubu ne ya amince da nadin Arabi a matsayin Shugaban Hukumar NAHCON a ranar 17 ga watan Oktoban 2023.

 

Daga cikin muhimman abubuwan da tarihi ba zai manta da ambaton sunan Arabi ba, sun haɗa da:

1. Samun Biza cikin sauki: Duk wani mahajjaci ya samu bizarsa ne kafin fara jigilar alhazai.

2. Ayyukan jigilar mahajjata zuwa Saudiyya: Sama da Alhazai 52,000 ne aka kwashe kafin ranar 9 ga watan Yunin 2024, kafin cikar wa’adin da Saudiyya ke bai wa kasashe na kammala jigilar alhazai. Kuma an kammala jigilar dawo da alhazai gida Nijeriya da kwanaki biyar saura.

3. Jin dadin Alhazai a Mina: An raba kayayyakin jin dadi kamar kayan zuwa bayan gida da karamar fankar hannu don maganin zafi.

4. Kula da kiwon Lafiya: An bayar da magunguna kyauta na cututtukan da ake saurin kamuwa kamar zazzabin cizon sauro da hawan jini, tare da tabbatar da kulawa da mahajjata cikin gaggawa akan lokaci.

 

Wadannan nasarori, da aka cimma duk da kalubalen tattalin arziki, sun nuna jajircewa da sadaukarwar NAHCON. Ƙoƙarin Jalal Arabi ya sami karɓuwa a duniya a lokacin da aka keɓe shi aka ba shi damar shiga wani ɓangare a Ka’aba mai tsarki wanda aka keɓe ga fitattun mutane a duniya.

 

A yayin da NAHCON ke ci gaba da samun nasarori, aikin Hajji na 2025 ya shirya tsaf don samun nasara tare da gudanar da aikin hajji cikin sauki ga mahajjatan Nijeriya. Irin wannan shine amfanin kafa tushe mai ƙarfi.

Hajjin 2024
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Hajjin 2024
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ba a Tsawaita Ranar 31 Ga Oktoba Ba Ta Dawowar Jakadun Nijeriya Gida – Minista
Sharhi

Yadda Tuggar Ya Sabunta Harkokin Diflomasiyyar Nijeriya

April 9, 2026
Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON
Sharhi

Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON

December 17, 2025
Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa
Sharhi

Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa

May 17, 2024
Next Post
Hajjin 2024

Muhimman Abubuwan Da Suka Faru A Masana’antar Fina-finan Nijeriya A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.