ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bitar Aikin Hajjin 2024

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Hajjin 2024

Aikin Hajjin 2024, ya ajiye tarihin da ba za a manta da shi ba a tarihin aikin hajjin da Nijeriya ta halarta a kasar Saudiyya ta fuskoki da dama sakamakon tsare-tsaren da Hukumar jin dadin alhazai ta kasa, NAHCON ta aiwatar.

 

NAHCON, a karkashin jagorancin Malam Jalal Ahmad Arabi ta samu nasarori da yabo daga mahajjata da masu sanya ido a harkokin aikin hajji bisa aiwatar da tsare-tsaren kwarewa da hukumar ke da shi a tarihinta. Sai dai ana cewa, Ubangiji ne kadai ya cika 100 bisa 100.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Lalata Matatun Mai 20 A Yankin Niger Delta
  • Yadda Mai Haihuwar Fari Za Ta Kula Da Kanta (2)

Kwararren masanin aikin Hajji, Ustaz Abubakar Siddeq Muhammad, a cikin sharhinsa mai suna “Mal. Jalal Ahmad Arabi a aikin Hajjin 2024 (2)” wanda Kamfanin jaridar LEADERSHIP ya buga, ya yaba da tsare-tsaren shirye-shiryen Arafah da ba a taba yin irinsa ba inda ya ce. “A karon farko cikin fiye da shekaru 20, an shirya tantunan Nijeriya tsaf, an baje shimfidar kafet da na’urorin sanyi,” in ji shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Tuggar Ya Sabunta Harkokin Diflomasiyyar Nijeriya

Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON

Bugu da kari, wani masanin ayyukan aikin hajji, ya yi sharhi da tsokaci game da nasarorin da Arabi ya samu a lokacin jagorancinsa a matsayin shugaban hukumar NAHCON, kamar yadda aka buga a: “https://www.hajjnews.com.ng/2024/12/nahcon-in-2024-year-of-achievements-challenges-and-renewal.html”

 

Duk da cewa, rayuwa ba matabbata ba ce, haka ma, mulki ko jagoranci, suna da lokaci da iyaka. An yanke wa’adinsa jagorancinsa saboda wasu dalilai na siyasa da zarge-zarge amma shugabancin Jalal Arabi a matsayin Shugaban Hukumar NAHCON ya ba da sakamako wanda ya kawo sauyi, wanda a halin yanzu ke tabbace cikin cikakken bayanin rahoton Hukumar na 2024, mai taken “2024: Shekarar Nasarori, Kalubale, da Sabuntawa”.

 

Shugaban kasa, Bola Tinubu ne ya amince da nadin Arabi a matsayin Shugaban Hukumar NAHCON a ranar 17 ga watan Oktoban 2023.

 

Daga cikin muhimman abubuwan da tarihi ba zai manta da ambaton sunan Arabi ba, sun haɗa da:

1. Samun Biza cikin sauki: Duk wani mahajjaci ya samu bizarsa ne kafin fara jigilar alhazai.

2. Ayyukan jigilar mahajjata zuwa Saudiyya: Sama da Alhazai 52,000 ne aka kwashe kafin ranar 9 ga watan Yunin 2024, kafin cikar wa’adin da Saudiyya ke bai wa kasashe na kammala jigilar alhazai. Kuma an kammala jigilar dawo da alhazai gida Nijeriya da kwanaki biyar saura.

3. Jin dadin Alhazai a Mina: An raba kayayyakin jin dadi kamar kayan zuwa bayan gida da karamar fankar hannu don maganin zafi.

4. Kula da kiwon Lafiya: An bayar da magunguna kyauta na cututtukan da ake saurin kamuwa kamar zazzabin cizon sauro da hawan jini, tare da tabbatar da kulawa da mahajjata cikin gaggawa akan lokaci.

 

Wadannan nasarori, da aka cimma duk da kalubalen tattalin arziki, sun nuna jajircewa da sadaukarwar NAHCON. Ƙoƙarin Jalal Arabi ya sami karɓuwa a duniya a lokacin da aka keɓe shi aka ba shi damar shiga wani ɓangare a Ka’aba mai tsarki wanda aka keɓe ga fitattun mutane a duniya.

 

A yayin da NAHCON ke ci gaba da samun nasarori, aikin Hajji na 2025 ya shirya tsaf don samun nasara tare da gudanar da aikin hajji cikin sauki ga mahajjatan Nijeriya. Irin wannan shine amfanin kafa tushe mai ƙarfi.

Hajjin 2024
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Hajjin 2024
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Ba a Tsawaita Ranar 31 Ga Oktoba Ba Ta Dawowar Jakadun Nijeriya Gida – Minista
Sharhi

Yadda Tuggar Ya Sabunta Harkokin Diflomasiyyar Nijeriya

April 9, 2026
Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON
Sharhi

Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON

December 17, 2025
Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa
Sharhi

Sarkin Lafiya Ya Hada Kan Sarakunan Nasarawa Ba Bambanci – Zanwa

May 17, 2024
Next Post
Hajjin 2024

Muhimman Abubuwan Da Suka Faru A Masana’antar Fina-finan Nijeriya A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.