Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Yadda Ministar Mata, Pauline Tallen, Ta Kamu Da Cutar Korona

by Muhammad
December 28, 2020
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Tallen
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya,

Ministar kula da harkokin mata a Nijeriya, Madam Pauline Tallen ta kamu da cutar murar mashako, wato cutar Korona.
Tallen ta bayyana wannan batun ne a wani jawabin da ta fitar a jiya Lahadi. Ta na mai shaida cewar ta amshi shawarar jami’an lafiya ne bayan da ta gana da wasu mutane da aka gano sun kamu da cutar Korona da har ta fara nunawa a jikinsu.
Jawabin nata na cewa, “Biyo bayan mu’amala da wasu daidaikun mutane da na yi wadanda suka kamu da korona; jami’an lafiya sun shawarce ni da na yi gwaji kana na illace kaina na ‘yan wasu kwanaki.
“Ina sanar da jama’a cewa bayan da aka yi min gwaji ni da iyalaina, sakamakon gwajina ya fito ya nuna cewa tabbas na kamu da cutar Korona, yayin da su kuma sauran iyalaina nasu sakamakon ya nuna cewa ba su kamu da cutar ba.
“A yanzu haka na shiga kulle domin jinyar cutar nan ta Korona tare da amsar magunguna. Don Allah ina rokon addu’o’inku, kuma ina rokonku da ku kasance masu yarda da ce Korona gaskiya ce, ku kula da matakan kariya daga kamuwa da wannan annobar.
“Ina rokonku da ku kula da kawukanku da na iyalanku tare da kasarmu,” a cewar Ministan.
Ministar ta yi fatan alkairi da addu’ar Allah kawo karshen wannan cutar ta Korona mai hanzarin yaduwa a tsakanin jama’a, inda ta hori ‘yan Nijeriya da su kasance masu bin matakan kariyan kai daga kamuwa da wannan cutar ta Korona.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Yi Alhinin Rasuwar Garkuwan Gombe, Sanata Kumo 

Next Post

An Cafke Hakimi Da Mutum 10 Bisa Fashi Da Makami A Neja

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Muhammad
8 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Muhammad
8 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Muhammad
8 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Nairobi

An Cafke Hakimi Da Mutum 10 Bisa Fashi Da Makami A Neja

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version