Yayin da ‘yan Nijeriya ke jiran sanarwar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), na fitar da jaddawalin harkokin siyasa gabanin zaben 2027, kasa da jihohi 10 da manyan jam’iyyun siyasa a kasar nan da suka bayyana shirinsu na gudanar da zaben fid da gwani.
Mafi yawancin jam’iyyun a jihohin kamar APC, PDP, LP da NNPP, na fuskantar manyan rikice-rikice da suka ki ci suka ki cinyewa.
- Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba
- Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Rarrabewar da ta fara bayan kammala zaben 2023, duk da irin kokarin shawo kan rikice-rikicen amma hakan ya ci tura. A wasu jihohi, akwai fargaba cewa jam’iyyun na iya shiga zaben 2027 cikin rarrabuwar kawuna.
Jihohin da ke fama da rikice-rikicen jam’iyyun sun hada da Benuwai (APC, PDP); Katsina (PDP); Zamfara (APC); Kano (NNPP); Jigawa (PDP); Ribas (APC, PDP); Bayelsa (PDP); Neja (APC); Oyo (APC); Abiya (LP); Kwara (APC); Bauchi (APC); Ogun (APC).
Ga jam’iyyun adawa, rikicin a matakin kasa na jam’iyyunsu ya kara dagula lamura ga manyan masu rike da mukami, wanda ya sa kowa yana takansa.
A wasu lokuta, matsalolin suna fitowa kai tsaye sakamakon rashin fahimta daga mataki na kasa, wadada a wasu lokutan ba su da wata alaka da sakatariyar jam’iyyun da ke mataki na sama.
Ko a cikin jam’iyyar APC da ke mulki, akwai jayayya a cikin rassan jihohinta da ba su warware ba kuma suna barazanar ga damar jam’iyyar a jihohin da abin ya shafa.
Wasu masana harkokin siyasa sun bayyana cewa rarrabuwar kawunan ta samu ne sakamakon nuna iko tsakanin wasu mutane a wasu jihohi. Akwai batun wanda ke da iko da tsarin jam’iyyar shi ne shugaban jam’iyyar a jihar.
Yayin da wasu ke cewa wannan shi ne tushen da ya haifar da rarrabuwar kawuna da ke faruwa a cikin tsarin jam’iyyun a jihohi, inda jiga-jigan ‘yan siyasa ke ta kokarin mallakar masu ruwa da tsaki na jam’iyya ta yadda za sus amu damar kulawa da jam’iyyun a jihohinsu.
Masana harkikin siyasa na ganin cewa idan har abubuwa ba su Sanya ba, to za a fuskanci matsaloli a tsakanin mambobin jam’iyya a lokacin zaben fid da gwani, wanda hakan na iya shafar zaben 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp