ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

by Sadiq
4 years ago
Kwari

‘Yan kasuwar Kantin Kwari a Jihar Kano sun koka kan asarar dukiyoyi da suka yi sakamakon ambaliyar ruwa.

Wannan na dauke me cikin wata tattaunawa da LEADERSHIP Hausa ta yi da ‘yan kasuwar, inda suka ce ‘yan kasuwa da dama suna kwashe kayayyakin da ke shagunansu.

  • Masarautar Bwari Jiya Da Yau
  • Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

Rahoton ya nuna cewa, ambaliyar ta afku ne bayan da aka yi ruwan sama kamar da bakin kwarya a daren ranar Laraba, yayin da aka toshe mafi yawan magudanan ruwa a kasuwar.

ADVERTISEMENT

Wasu daga cikin ‘yan kasuwar da suka zanta da wakilinmu, sun danganta lamarin da rashin magudanan ruwa, da gina hanyoyin ruwa da kuma sabuwar gadar sama da aka gina a kusa da kasuwar.

Sun yi kira ga gwamnati da ta kawo musu dauki domin sun yi asarar kayayyakin na miliyoyin Naira.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Kwamared Balarabe Tatari, shi ne shugaban kungiyar ‘yan kasuwa kanana da matsakaita na kantin kwarin, ya yi magana kan yadda suka yi hasashen faruwar irin wannan yanayi a lokacin da aka gina sabbin gine-gine a layin Ta’anbo da kuma layin Bayajidda.

Ya ci gaba da cewa, duk kokarin da kungiyar ta yi don ganin an yi wani abu game da lamarin ya ci tura. Ya ce rashin tsarin sufuri da hanyoyin ruwa a cikin kasuwar ya taimaka wajen ambaliya da sauran haduran muhalli.

Alhaji Balarabe ya bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki da su taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da daukar matakin da ya dace domin dakile faruwar lamarin nan gaba.

A halin da ake ciki, shugaban hukumar da ke kula da Kantin Kwari, Alhaji Abba Muhammad Bello ya musanta cewa gine-ginen sun toshe hanyoyin ruwa.

Ya ce an rufe wasu magudanun ruwa ne na wani dan lokaci saboda aikin da ake yi a kasuwar.

Ya jaddada cewa hukumar za ta mika cikakken rahoto ga gwamnati domin daukar matakin da ya dace.

Idan za a iya tunawa, a watan Agustan 2021, ‘yan kasuwa a kasuwar Kantin Kwari sun gudanar da zanga-zangar lumana don nuna rashin gamsuwarsu da wani gini da ake ginawa a Layin Ta’anbo a cikin kasuwar.

Sun yi nuni da cewa layin Ta’anbo na daya daga cikin hanyoyin da ake amfani da su wajen safarar kayayyaki a cikin kasuwar sannan tasha ce da ke hada magudanun ruwa.

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
hadeja

Mai Martaba Sarkin Hadeja Zai Cika Shekara 20 Kan Karaga

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.