• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
ASUU

Majalisar Dattawa ta shiga tsakani don warware rikici tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyar malaman jami’o’i (ASUU), a wani yunƙuri na kawo ƙarshen yajin aikin gargaɗi na makonni biyu da malaman jami’ar ke yi.

A sakamakon haka, kwamitocin Majalisar Dattawa kan Kwadago da kuma Ilimi mai zurfi za su gana da Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, da Sakatare-Janar na hukumar Jami’o’i ta ƙasa (NUC), Farfesa Abdullahi Yusuf Ribadu, a ranar Talata mai zuwa.

  • Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
  • Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Wannan ganawa ta biyo bayan taron da kwamitocin suka gudanar da shugabannin ASUU a majalisar a ranar Juma’a, inda suka tattauna kan hanyoyin da za su bi don magance matsalolin da suka janyo yajin aikin. Shugaban kwamitin kan Ilimi mai zurfi da TETFund, Sanata Muntari Dandutse. ya bayyana wa manema labarai cewa sun saurari ƙorafe-ƙorafen ASUU kuma za su gabatar da su ga hukumomin da abin ya shafa.

A nasa jawabin kafin taron sirrin, shugaban ASUU na ƙasa, Farfesa Christopher Piwuna, ya ce buƙatar ƙungiyar ita ce gwamnati ta inganta kuɗaɗen gudanar da jami’o’i kamar yadda aka amince a yarjejeniyoyin baya. Ya bayyana cewa zuba jari mai ɗorewa a fannin ilimi ne kaɗai zai kawo ƙarshen yajin aiki da kuma ƙara matsayi ga jami’o’in Nijeriya a matakin duniya.

Farfesa Piwuna ya ce ASUU ta shafe shekaru takwas tana tattaunawa da gwamnati ba tare da sakamako mai gamsarwa ba, inda ya ambaci rahoton kwamitin Yayale Ahmed na Disamba 2024 da aka yi watsi da shi har sai bayan da yajin aikin ya fara. Ya kuma bayyana cewa daga cikin Naira biliyan 150 da majalisar ta amince da su domin jami’o’i, Naira biliyan 50 kawai aka saki, kuma tana maƙale a ma’aikatar ilimi. Ya gargaɗi gwamnati da kada ta karkatar da kuɗin zuwa wasu cibiyoyi kamar kwalejoji da polytechnic, domin an ware su ne musamman don jami’o’i.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Next Post
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.