• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan APC Ne Ke Ruruta Wutar Sai Ayu Ya Sauka –Dino Melaye

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan APC Ne Ke Ruruta Wutar Sai Ayu Ya Sauka –Dino Melaye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, Sanata Dino Melaye ya bayyana cewa ‘yan APC ne ke kara ruruwa wutar rikicin sai an cire shugaban jam’iyyar PDP, Dakta Iyorchia Ayu kafin zaben 2023.

Melaye ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa a dakin watsa shirye-shirye na LEADERSHIP da ke Abuja.

  • Kotu Ta Soke Takarar Dare A Matsayin Wanda Zai Yi Wa PDP Takarar Gwamna A Zamfara

Ya kara da cewa ‘yan APC suna kokarin tarwatsa tsarin mulkin jam’iyyar PDP, shi ya sa suka dage a kan sai an saukar da Ayu daga mukaminsa.

Melaye ya koka kan yadda jam’iyyar PDP ta samu kanta a rikicin cikin gida, amma duk da haka yana da tabbacin cewa Atiku ne zai lashe zaben shugaban kasa na 2023.

Shi dai Ayu ya ki amincewa da bukatar Gwamna Jihar Ribas, Nyesom Wike na ya sauka daga shugabancin jam’iyyar a matsayin sharadi da zai mara wa Atiku baya a zaben 2023.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Ya ce, “Wadanda suka dage sai an cire Ayu daga shugabancin PDP, ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke kokarin tarwatsa tsarin mulkin PDP domin APC ta amfana.

“Idan muka duba tsarin mulkin jam’iyyarmu, in har aka cire shugaban jam’iyyar, to dole a maye gurbinsa da wani da suke yankin daya. A yau idan har Ayu ya sauka, mataimakinsa daga yankin arewa ne zai gaje shi.

“Kuma suna adawa ne kan dan arewa bai kamata ya zama shugaban jam’iyyar ba, sannan dan takarar shugaban kasa ya kasance dan arewa, amma hakan ya taba faruwa a baya lokacin da dan arewa yake shugabancin jam’iyyar aka zabi Goodluck Jonathan, sa’ilin da aka rantsar da Jonathan sai aka cire shi nan take.

“Mu ba mu ce Ayu ya ci gaba da shugabancin jam’iyyar lokacin da aka zabi Atiku a matsayin shugaban kasa ba. Lokacin da Atiku ya samu nasara a zabe, to dole Ayu ya sauka daga shugabancin jam’iyyar.

“Lokacin da muka zabi Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar, kowa ya san daga yankin Arewa ya fito, an dai zabe shi ne bisa cancanta da zai iya magance matsalolin jam’iyyar.
“Bisa haka, nake cewa babu wata matsala. Jam’iyyar PDP ta kasance tana da kyakkyawan tsari da muke tabbatar da cewa kowa ana ba shi hakkinsa,” in ji shi.
Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Atiku ya dage da cewa dan karamin rashin jituwa ne aka samu tsakanin bangarori guda biyu na jam’iyyar wanda ake samu a cikin harkokin dimokuradiyya.
A cewarsa, matsala da aka samu da Wike nan da ‘yan kwanaki komai zai daidaita, domin ita PDP jam’iyya ce mai hada kan ‘ya’yanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

Next Post

Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen VC Na Jami’ar Bayero Ta Kano 

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen VC Na Jami’ar Bayero Ta Kano 

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

July 1, 2025
Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

July 1, 2025
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

July 1, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci

Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci

July 1, 2025
Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

July 1, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

July 1, 2025
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.