ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan APC Ne Ke Ruruta Wutar Sai Ayu Ya Sauka –Dino Melaye

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
APC

Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, Sanata Dino Melaye ya bayyana cewa ‘yan APC ne ke kara ruruwa wutar rikicin sai an cire shugaban jam’iyyar PDP, Dakta Iyorchia Ayu kafin zaben 2023.

Melaye ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa a dakin watsa shirye-shirye na LEADERSHIP da ke Abuja.

  • Kotu Ta Soke Takarar Dare A Matsayin Wanda Zai Yi Wa PDP Takarar Gwamna A Zamfara

Ya kara da cewa ‘yan APC suna kokarin tarwatsa tsarin mulkin jam’iyyar PDP, shi ya sa suka dage a kan sai an saukar da Ayu daga mukaminsa.

ADVERTISEMENT

Melaye ya koka kan yadda jam’iyyar PDP ta samu kanta a rikicin cikin gida, amma duk da haka yana da tabbacin cewa Atiku ne zai lashe zaben shugaban kasa na 2023.

Shi dai Ayu ya ki amincewa da bukatar Gwamna Jihar Ribas, Nyesom Wike na ya sauka daga shugabancin jam’iyyar a matsayin sharadi da zai mara wa Atiku baya a zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Ya ce, “Wadanda suka dage sai an cire Ayu daga shugabancin PDP, ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke kokarin tarwatsa tsarin mulkin PDP domin APC ta amfana.

“Idan muka duba tsarin mulkin jam’iyyarmu, in har aka cire shugaban jam’iyyar, to dole a maye gurbinsa da wani da suke yankin daya. A yau idan har Ayu ya sauka, mataimakinsa daga yankin arewa ne zai gaje shi.

“Kuma suna adawa ne kan dan arewa bai kamata ya zama shugaban jam’iyyar ba, sannan dan takarar shugaban kasa ya kasance dan arewa, amma hakan ya taba faruwa a baya lokacin da dan arewa yake shugabancin jam’iyyar aka zabi Goodluck Jonathan, sa’ilin da aka rantsar da Jonathan sai aka cire shi nan take.

“Mu ba mu ce Ayu ya ci gaba da shugabancin jam’iyyar lokacin da aka zabi Atiku a matsayin shugaban kasa ba. Lokacin da Atiku ya samu nasara a zabe, to dole Ayu ya sauka daga shugabancin jam’iyyar.

“Lokacin da muka zabi Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar, kowa ya san daga yankin Arewa ya fito, an dai zabe shi ne bisa cancanta da zai iya magance matsalolin jam’iyyar.
“Bisa haka, nake cewa babu wata matsala. Jam’iyyar PDP ta kasance tana da kyakkyawan tsari da muke tabbatar da cewa kowa ana ba shi hakkinsa,” in ji shi.
Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Atiku ya dage da cewa dan karamin rashin jituwa ne aka samu tsakanin bangarori guda biyu na jam’iyyar wanda ake samu a cikin harkokin dimokuradiyya.
A cewarsa, matsala da aka samu da Wike nan da ‘yan kwanaki komai zai daidaita, domin ita PDP jam’iyya ce mai hada kan ‘ya’yanta.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.