• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga: Gwamna Dauda Ya Kai Ziyarar Jaje A Zurmi Da Birnin Magaji

by Leadership Hausa
2 years ago
in Adon Gari
0
‘Yan Bindiga: Gwamna Dauda Ya Kai Ziyarar Jaje A Zurmi Da Birnin Magaji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal a Juma’ar nan ya ziyarci al’ummomin Ƙananan Hukumomin Zurmi da Birnin Magaji bisa harin ta’addancin da ‘yan bindiga suka kai, inda Gwamnan ya jaddada aniyarsa ta kawo ƙarshen matsalar tsaron da jihar ke fama da shi.

In dai ba a manta ba, a makon da ya gabata ne ‘yan bindiga suka kai hare-hare a Nassarawar Zurmi da ke Ƙaramar Hukumar Zurmi da Nasarawar Godel da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji a cikin jihar ta Zamfara.

A sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu a Gusau, ya bayyana cewa ziyarar ta kasance ta jaje ce da ta’aziyya ga al’ummar da wannan bala’i ya shafa na asarar rayuka, tare da nuna cewa gwamnati na tare da su.

Ya ce, Gwamnan ya nuna wa jama’ar cewa yana tare da su, ya kuma tabbatar da jajircewar gwamnatinsa wajen lalubo sahihiyar hanyar kawo ƙarshen wannan bala’i da ya addabi jihar.

  • Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci

 

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Sanarwar ta Malam Idris ta kuma bayyana cewa, a yayin da Gwamna Dauda ya kai ziyarar gani da ido ga ofishin ‘yan sanda na Zurmi, wanda ‘yan ta’addan suka ƙona, ya nuna masu a shirye yake wajen samar masu da duk kayan aikin da suke nema don wannan namijin aiki.

Gwamna Lawal ya ce, “Ina miƙa saƙon ta’aziyya ta game da jami’ai biyu da suka rasa rayukansu a harin da ‘yan bindiga suka kai wa Nasarawar Zurmi. Ina sane da irin tashin hankalin da ke tattare da irin wannan bala’i ga duk wanda ta rutsa da shi, ina tabbatar maku, tare da iyalan waɗannan gwaraza, cewa ina tare da duk al’ummar wannan yanki a cikin addu’o’i na.

“Na yi matuƙar jinjina ga ƙoƙarin jajirtattun jami’an tsaronmu masu yaƙi da ta’addanci. Jajircewar ku na ganin kun kare al’ummar mu daga ‘yan ta’adda, wannan abin yabawa ne.

“Gwamnati na za ta ci gaba da bayar da duk wani taimako da dakarun muke buƙata. Tare za mu kawo ƙarshen waɗannan matsaloli, kuma mu ƙara ƙarfi.”

A lokacin da Gwamna Lawal ya shiga garin Zurmi, ya kai gaisuwar ban-girma ga Sarkin Zurmi, Alhaji Bello Sulaiman.

Da yake jawabi ga jama’ar Nasarawar Godal da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji kuwa, Gwamna Lawal ya tabbatar masu da cewa ya riga ya aiko da kayan tallafi tun lokacin da abin ya faru.

“Na zo yau ne domin in nuna tausayawa ta da ta’aziyya ga iyalan waɗanda wannan abu ya shafa, tare da tabbatar da cewa gwamnati na ba za ta numfasa ba, har sai ta kawo ƙarshen wannan rashin tsaro.

“Ina fata wannan ziyara tawa za ta miƙa wani saƙon kyakkywar fata ga al’ummar Nasarawar, tare da tabbatar masu da cewa muna tare da su a wannan mawiyacin hali.

A lokacin da ya ke dawowa zuwa Gusau, Gwamna Lawal ya yada zango a Kasuwar Daji da ke Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda don jajanta wa Alhaji Hamisu Kasuwar Daji, wanda waɗannan ‘yan ta’adda suka kai wa gidansa hari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: birnin magajiGwamna Dauda LawalTsaroYan bindigaZamfaraZurmi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekaru 2 Ke Nan Da Barkewar Rikici A Tsakanin Rasha Da Ukraine

Next Post

Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

Related

tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

2 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

1 month ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

2 months ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

4 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

4 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

7 months ago
Next Post
Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

LABARAI MASU NASABA

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

September 11, 2025
Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.