ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe

by Sadiq
3 years ago
Benuwe

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane uku a wasu hare-hare da suka kai wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Guma da ke jihar Benuwe.

Hakan dai ya zo ne kwanaki uku da kashe mutane biyar da suka hada da wani malamin cocin Katolika da matarsa a kauyukan karamar hukumar Guma.

  • Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato
  • Shugaban PDP Na Shiyyar Kudu Maso Yamma, Adagunodo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 62

Mazauna kauyen sun ce harin na baya-bayan ya auku ne da yammacin ranar Litinin a kauyen Tse-Vambe da ke gundumar Mbagwa da kuma yankin Tse-Iortim Torough Mbanyiar, duk a Guma.

ADVERTISEMENT

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa mutane uku ne suka mutu a harin da wasu mahara dauke da makamai suka kai tare da jikkata wasu da dama.

Mai ba da shawara kan harkokin tsaro na karamar hukumar Guma, Christopher Waku, wanda ya tabbatar wa manema labarai harin a Makurdi, ya ce an kashe mutane uku.

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

“An kashe mutum daya a Tse Vambe kuma an kashe wasu biyu a yankin Tse Iortim wanda ya zama uku,” in ji shi.

Waku ya nuna damuwarsa kan yadda kusan dukkanin sassan karamar hukumar kwanan nan suka fuskanci kawanya daga wasu mahara dauke da makamai wadanda kuma suka mamaye ko ina da shanunsu.

Ya kara da cewa, “Mun ga su (makiyaya) a ko ina; an kusa kwace garin Guma gaba daya. Mun gansu da yawansu a Yogbo wacce ita ce gundumar Mbayer/Yandev, tun daga Yelwata har zuwa Ukohol, a Ortese da Hirnyam, inda aka kashe mutane a ranar Juma’ar da ta gabata.

“Suna cikin adadinsu a Uvir da Nzorov; karamar hukumar gwamna. A gaskiya ma, a Nzorov, akwai makiyaya da yawa a can da shanunsu, irin su Mbawa, Mbadwem, Mbabai da sauransu.

“Idan mutane suka je gona a yanzu, za su kashe su ne kawai. Suna tilastawa mutane barin gidajensu da tushen rayuwarsu. A makon da ya gabata, Catechist da matarsa suna cikin gidansu lokacin da mahara suka zo suka kashe su. Idan mutane suna kwancr a gidajensu sai kawai su zo su kashe su… wannan aikin dabbanci ne.”

Da aka tuntubi kakakin ‘yansandan jihar Benuwe, SP Catherine Anene, ta ce har yanzu ba ta samu rahoton faruwar lamarin ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
Labarai

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Labarai

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

'Yansanda Sun Hallaka 'Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.