• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane uku a wasu hare-hare da suka kai wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Guma da ke jihar Benuwe.

Hakan dai ya zo ne kwanaki uku da kashe mutane biyar da suka hada da wani malamin cocin Katolika da matarsa a kauyukan karamar hukumar Guma.

  • Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato
  • Shugaban PDP Na Shiyyar Kudu Maso Yamma, Adagunodo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 62

Mazauna kauyen sun ce harin na baya-bayan ya auku ne da yammacin ranar Litinin a kauyen Tse-Vambe da ke gundumar Mbagwa da kuma yankin Tse-Iortim Torough Mbanyiar, duk a Guma.

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa mutane uku ne suka mutu a harin da wasu mahara dauke da makamai suka kai tare da jikkata wasu da dama.

Mai ba da shawara kan harkokin tsaro na karamar hukumar Guma, Christopher Waku, wanda ya tabbatar wa manema labarai harin a Makurdi, ya ce an kashe mutane uku.

Labarai Masu Nasaba

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

“An kashe mutum daya a Tse Vambe kuma an kashe wasu biyu a yankin Tse Iortim wanda ya zama uku,” in ji shi.

Waku ya nuna damuwarsa kan yadda kusan dukkanin sassan karamar hukumar kwanan nan suka fuskanci kawanya daga wasu mahara dauke da makamai wadanda kuma suka mamaye ko ina da shanunsu.

Ya kara da cewa, “Mun ga su (makiyaya) a ko ina; an kusa kwace garin Guma gaba daya. Mun gansu da yawansu a Yogbo wacce ita ce gundumar Mbayer/Yandev, tun daga Yelwata har zuwa Ukohol, a Ortese da Hirnyam, inda aka kashe mutane a ranar Juma’ar da ta gabata.

“Suna cikin adadinsu a Uvir da Nzorov; karamar hukumar gwamna. A gaskiya ma, a Nzorov, akwai makiyaya da yawa a can da shanunsu, irin su Mbawa, Mbadwem, Mbabai da sauransu.

“Idan mutane suka je gona a yanzu, za su kashe su ne kawai. Suna tilastawa mutane barin gidajensu da tushen rayuwarsu. A makon da ya gabata, Catechist da matarsa suna cikin gidansu lokacin da mahara suka zo suka kashe su. Idan mutane suna kwancr a gidajensu sai kawai su zo su kashe su… wannan aikin dabbanci ne.”

Da aka tuntubi kakakin ‘yansandan jihar Benuwe, SP Catherine Anene, ta ce har yanzu ba ta samu rahoton faruwar lamarin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BenuweGumaHariYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Next Post

‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

Related

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

55 minutes ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

2 hours ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

11 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

12 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

13 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

14 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

'Yansanda Sun Hallaka 'Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.