• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane uku a wasu hare-hare da suka kai wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Guma da ke jihar Benuwe.

Hakan dai ya zo ne kwanaki uku da kashe mutane biyar da suka hada da wani malamin cocin Katolika da matarsa a kauyukan karamar hukumar Guma.

  • Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato
  • Shugaban PDP Na Shiyyar Kudu Maso Yamma, Adagunodo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 62

Mazauna kauyen sun ce harin na baya-bayan ya auku ne da yammacin ranar Litinin a kauyen Tse-Vambe da ke gundumar Mbagwa da kuma yankin Tse-Iortim Torough Mbanyiar, duk a Guma.

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa mutane uku ne suka mutu a harin da wasu mahara dauke da makamai suka kai tare da jikkata wasu da dama.

Mai ba da shawara kan harkokin tsaro na karamar hukumar Guma, Christopher Waku, wanda ya tabbatar wa manema labarai harin a Makurdi, ya ce an kashe mutane uku.

Labarai Masu Nasaba

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

“An kashe mutum daya a Tse Vambe kuma an kashe wasu biyu a yankin Tse Iortim wanda ya zama uku,” in ji shi.

Waku ya nuna damuwarsa kan yadda kusan dukkanin sassan karamar hukumar kwanan nan suka fuskanci kawanya daga wasu mahara dauke da makamai wadanda kuma suka mamaye ko ina da shanunsu.

Ya kara da cewa, “Mun ga su (makiyaya) a ko ina; an kusa kwace garin Guma gaba daya. Mun gansu da yawansu a Yogbo wacce ita ce gundumar Mbayer/Yandev, tun daga Yelwata har zuwa Ukohol, a Ortese da Hirnyam, inda aka kashe mutane a ranar Juma’ar da ta gabata.

“Suna cikin adadinsu a Uvir da Nzorov; karamar hukumar gwamna. A gaskiya ma, a Nzorov, akwai makiyaya da yawa a can da shanunsu, irin su Mbawa, Mbadwem, Mbabai da sauransu.

“Idan mutane suka je gona a yanzu, za su kashe su ne kawai. Suna tilastawa mutane barin gidajensu da tushen rayuwarsu. A makon da ya gabata, Catechist da matarsa suna cikin gidansu lokacin da mahara suka zo suka kashe su. Idan mutane suna kwancr a gidajensu sai kawai su zo su kashe su… wannan aikin dabbanci ne.”

Da aka tuntubi kakakin ‘yansandan jihar Benuwe, SP Catherine Anene, ta ce har yanzu ba ta samu rahoton faruwar lamarin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BenuweGumaHariYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Next Post

‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

Related

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye
Manyan Labarai

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

41 minutes ago
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i
Labarai

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

3 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a
Manyan Labarai

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

4 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

13 hours ago
'yansanda
Labarai

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai
Labarai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

15 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

'Yansanda Sun Hallaka 'Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

September 9, 2025
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

September 9, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.