• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Benuwe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane uku a wasu hare-hare da suka kai wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Guma da ke jihar Benuwe.

Hakan dai ya zo ne kwanaki uku da kashe mutane biyar da suka hada da wani malamin cocin Katolika da matarsa a kauyukan karamar hukumar Guma.

  • Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato
  • Shugaban PDP Na Shiyyar Kudu Maso Yamma, Adagunodo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 62

Mazauna kauyen sun ce harin na baya-bayan ya auku ne da yammacin ranar Litinin a kauyen Tse-Vambe da ke gundumar Mbagwa da kuma yankin Tse-Iortim Torough Mbanyiar, duk a Guma.

Mazauna yankin sun shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa mutane uku ne suka mutu a harin da wasu mahara dauke da makamai suka kai tare da jikkata wasu da dama.

Mai ba da shawara kan harkokin tsaro na karamar hukumar Guma, Christopher Waku, wanda ya tabbatar wa manema labarai harin a Makurdi, ya ce an kashe mutane uku.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

“An kashe mutum daya a Tse Vambe kuma an kashe wasu biyu a yankin Tse Iortim wanda ya zama uku,” in ji shi.

Waku ya nuna damuwarsa kan yadda kusan dukkanin sassan karamar hukumar kwanan nan suka fuskanci kawanya daga wasu mahara dauke da makamai wadanda kuma suka mamaye ko ina da shanunsu.

Ya kara da cewa, “Mun ga su (makiyaya) a ko ina; an kusa kwace garin Guma gaba daya. Mun gansu da yawansu a Yogbo wacce ita ce gundumar Mbayer/Yandev, tun daga Yelwata har zuwa Ukohol, a Ortese da Hirnyam, inda aka kashe mutane a ranar Juma’ar da ta gabata.

“Suna cikin adadinsu a Uvir da Nzorov; karamar hukumar gwamna. A gaskiya ma, a Nzorov, akwai makiyaya da yawa a can da shanunsu, irin su Mbawa, Mbadwem, Mbabai da sauransu.

“Idan mutane suka je gona a yanzu, za su kashe su ne kawai. Suna tilastawa mutane barin gidajensu da tushen rayuwarsu. A makon da ya gabata, Catechist da matarsa suna cikin gidansu lokacin da mahara suka zo suka kashe su. Idan mutane suna kwancr a gidajensu sai kawai su zo su kashe su… wannan aikin dabbanci ne.”

Da aka tuntubi kakakin ‘yansandan jihar Benuwe, SP Catherine Anene, ta ce har yanzu ba ta samu rahoton faruwar lamarin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BenuweGumaHariYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Next Post

‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

1 hour ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

3 hours ago
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

4 hours ago
Labarai

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

6 hours ago
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
Labarai

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

8 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

9 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

'Yansanda Sun Hallaka 'Yan Bindiga 3, Sun Kwato Bindigogi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.