ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda, Sun Sace ‘Yan China 4 A Wajen Hakar Ma’adinai A Neja

by Sadiq
3 years ago
'Yan Bindiga

Akalla mutane 17 ne aka ruwaito sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka samu munanan raunuka bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a wani wajen hakar ma’adanai da ‘yan kasar China suke gudanarwa a Ajata-Aboki a unguwar Gurmana na karamar hukumar Shiroro a Jihar Neja.

Rahotannin sun ce an kai harin ne da yammacin ranar Laraba inda aka kashe mutane bakwai da suka hada da ‘yan sandan da ke gadin masu hakar ma’adinai da ma’aikata.

  • 2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose
  • Wata Tawagar ‘Yan PDP Sun Koma APC A Jihar Osun

An ce maharan dauke da muggan makamai, sun isa unguwar ne da misalin karfe 2 na rana, inda suka nufi wajen da ake hakar ma’adinan, sannan suka bude wuta.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan tsaron cikin gida da jin kai na jihar, Emmanuel Umar, ya tabbatar da faruwar harin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, sai dai ya ce kawo yanzu ba a tantance adadin wadanda suka mutu ba.

Ya ce, “Gwamnatin Jihar Neja na son tabbatar da cewa a ranar 29/6/2022 da misalin karfe 2 na rana, bisa ga sanarwar da aka samu cewa ‘yan bindiga sun kai hari a wani wurin hakar ma’adinai da ke kauyen Ajata-Aboki ta gundumar Erena ta karamar hukumar Shiroro.

LABARAI MASU NASABA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

“An tura tawagar jami’an tsaro zuwa wurin domin kai dauki.”

Umar ya ce yayin da tawagar jami’an tsaro ta hadin gwiwa suka yi artabu da ‘yan bindigar, wanda ya yi sanadin asarar rayuka daga bangarorin biyu.

Ya kara da cewa, “Wani adadin ma’aikatan da ba a tantance ba a wurin hakar ma’adinan da suka hada da wasu ‘yan kasar China hudu an sace su.

“Jami’an tsaro sun hada karfi da karfe domin farautar sauran ‘yan bindigar tare da ceto wadanda suka jikkata ciki har da jami’an tsaro da suka samu raunuka daban-daban an kai su asibitin gwamnati da ke jihar domin yi musu magani.

“Yayin da gwamnatin jihar Neja ke jajantawa shugabannin hukumomin tsaro a jihar da kuma iyalan wadanda aka kashe, gwamnatin jihar ta ba da tabbacin cewa sadaukarwar da suka yi ba zai tafi a banza ba.”

Umar ya ce gwamnatin jihar ta amince da duk kokarin jami’an tsaro na hadin gwiwa da na al’ummomin jihar na ganin an shawo kan matsalar rashin tsaro a wasu sassan jihar.

Sai dai wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa “Kusan mutane 11 da suka hada da ‘yan sanda da mutane bakwai da ke aiki a wurin hakar ma’adinan da farar hula shida ne suka rasa rayukansu a harin.”

Ya ce an kai mutane da dama wadanda suka samu raunuka asibiti kuma suna cikin mawuyacin hali.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Next Post
An Yanke Wa Dan Sandan Da Ya Kashe Direban Bas Hukuncin Kisa

'Yan Bindiga Sun Kashe Mataimakin Sufeton 'Yan Sanda A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.