• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda, Sun Sace ‘Yan China 4 A Wajen Hakar Ma’adinai A Neja

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda, Sun Sace ‘Yan China 4 A Wajen Hakar Ma’adinai A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutane 17 ne aka ruwaito sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka samu munanan raunuka bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a wani wajen hakar ma’adanai da ‘yan kasar China suke gudanarwa a Ajata-Aboki a unguwar Gurmana na karamar hukumar Shiroro a Jihar Neja.

Rahotannin sun ce an kai harin ne da yammacin ranar Laraba inda aka kashe mutane bakwai da suka hada da ‘yan sandan da ke gadin masu hakar ma’adinai da ma’aikata.

  • 2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose
  • Wata Tawagar ‘Yan PDP Sun Koma APC A Jihar Osun

An ce maharan dauke da muggan makamai, sun isa unguwar ne da misalin karfe 2 na rana, inda suka nufi wajen da ake hakar ma’adinan, sannan suka bude wuta.

Kwamishinan tsaron cikin gida da jin kai na jihar, Emmanuel Umar, ya tabbatar da faruwar harin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, sai dai ya ce kawo yanzu ba a tantance adadin wadanda suka mutu ba.

Ya ce, “Gwamnatin Jihar Neja na son tabbatar da cewa a ranar 29/6/2022 da misalin karfe 2 na rana, bisa ga sanarwar da aka samu cewa ‘yan bindiga sun kai hari a wani wurin hakar ma’adinai da ke kauyen Ajata-Aboki ta gundumar Erena ta karamar hukumar Shiroro.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn

Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ɗaga Likafar Kwalejin Fasaha Ta Kabo Zuwa Jami’a

“An tura tawagar jami’an tsaro zuwa wurin domin kai dauki.”

Umar ya ce yayin da tawagar jami’an tsaro ta hadin gwiwa suka yi artabu da ‘yan bindigar, wanda ya yi sanadin asarar rayuka daga bangarorin biyu.

Ya kara da cewa, “Wani adadin ma’aikatan da ba a tantance ba a wurin hakar ma’adinan da suka hada da wasu ‘yan kasar China hudu an sace su.

“Jami’an tsaro sun hada karfi da karfe domin farautar sauran ‘yan bindigar tare da ceto wadanda suka jikkata ciki har da jami’an tsaro da suka samu raunuka daban-daban an kai su asibitin gwamnati da ke jihar domin yi musu magani.

“Yayin da gwamnatin jihar Neja ke jajantawa shugabannin hukumomin tsaro a jihar da kuma iyalan wadanda aka kashe, gwamnatin jihar ta ba da tabbacin cewa sadaukarwar da suka yi ba zai tafi a banza ba.”

Umar ya ce gwamnatin jihar ta amince da duk kokarin jami’an tsaro na hadin gwiwa da na al’ummomin jihar na ganin an shawo kan matsalar rashin tsaro a wasu sassan jihar.

Sai dai wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa “Kusan mutane 11 da suka hada da ‘yan sanda da mutane bakwai da ke aiki a wurin hakar ma’adinan da farar hula shida ne suka rasa rayukansu a harin.”

Ya ce an kai mutane da dama wadanda suka samu raunuka asibiti kuma suna cikin mawuyacin hali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ChinaHakar Ma'adinaiJami'an TsaroNejaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mataimakin Sufeton ‘Yan Sanda A Ribas

Related

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn

16 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ɗaga Likafar Kwalejin Fasaha Ta Kabo Zuwa Jami’a
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ɗaga Likafar Kwalejin Fasaha Ta Kabo Zuwa Jami’a

17 hours ago
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

1 day ago
Mai Unguwa
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wanda Ya Kona Masallata A Kano

2 days ago
Kakakin Majalisa Ya Janye Ƙudurin Dokar Tilastawa Ƴan Nijeriya Yin Zaɓe
Manyan Labarai

Kakakin Majalisa Ya Janye Ƙudurin Dokar Tilastawa Ƴan Nijeriya Yin Zaɓe

2 days ago
Rikici Ya Ɓarke Tsakanin ‘Yansanda Da Matasa A Rano, Mutum 1 Ya Mutu, An Harbi Wasu
Manyan Labarai

Rikici Ya Ɓarke Tsakanin ‘Yansanda Da Matasa A Rano, Mutum 1 Ya Mutu, An Harbi Wasu

2 days ago
Next Post
An Yanke Wa Dan Sandan Da Ya Kashe Direban Bas Hukuncin Kisa

'Yan Bindiga Sun Kashe Mataimakin Sufeton 'Yan Sanda A Ribas

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

May 27, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

May 27, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

May 27, 2025
Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

May 27, 2025
Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

May 27, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah

May 27, 2025
Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji

Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji

May 27, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC

May 27, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano

May 27, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 

May 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.