• English
  • Business News
Tuesday, July 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda, Sun Sace ‘Yan China 4 A Wajen Hakar Ma’adinai A Neja

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda, Sun Sace ‘Yan China 4 A Wajen Hakar Ma’adinai A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutane 17 ne aka ruwaito sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka samu munanan raunuka bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a wani wajen hakar ma’adanai da ‘yan kasar China suke gudanarwa a Ajata-Aboki a unguwar Gurmana na karamar hukumar Shiroro a Jihar Neja.

Rahotannin sun ce an kai harin ne da yammacin ranar Laraba inda aka kashe mutane bakwai da suka hada da ‘yan sandan da ke gadin masu hakar ma’adinai da ma’aikata.

  • 2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose
  • Wata Tawagar ‘Yan PDP Sun Koma APC A Jihar Osun

An ce maharan dauke da muggan makamai, sun isa unguwar ne da misalin karfe 2 na rana, inda suka nufi wajen da ake hakar ma’adinan, sannan suka bude wuta.

Kwamishinan tsaron cikin gida da jin kai na jihar, Emmanuel Umar, ya tabbatar da faruwar harin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, sai dai ya ce kawo yanzu ba a tantance adadin wadanda suka mutu ba.

Ya ce, “Gwamnatin Jihar Neja na son tabbatar da cewa a ranar 29/6/2022 da misalin karfe 2 na rana, bisa ga sanarwar da aka samu cewa ‘yan bindiga sun kai hari a wani wurin hakar ma’adinai da ke kauyen Ajata-Aboki ta gundumar Erena ta karamar hukumar Shiroro.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

“An tura tawagar jami’an tsaro zuwa wurin domin kai dauki.”

Umar ya ce yayin da tawagar jami’an tsaro ta hadin gwiwa suka yi artabu da ‘yan bindigar, wanda ya yi sanadin asarar rayuka daga bangarorin biyu.

Ya kara da cewa, “Wani adadin ma’aikatan da ba a tantance ba a wurin hakar ma’adinan da suka hada da wasu ‘yan kasar China hudu an sace su.

“Jami’an tsaro sun hada karfi da karfe domin farautar sauran ‘yan bindigar tare da ceto wadanda suka jikkata ciki har da jami’an tsaro da suka samu raunuka daban-daban an kai su asibitin gwamnati da ke jihar domin yi musu magani.

“Yayin da gwamnatin jihar Neja ke jajantawa shugabannin hukumomin tsaro a jihar da kuma iyalan wadanda aka kashe, gwamnatin jihar ta ba da tabbacin cewa sadaukarwar da suka yi ba zai tafi a banza ba.”

Umar ya ce gwamnatin jihar ta amince da duk kokarin jami’an tsaro na hadin gwiwa da na al’ummomin jihar na ganin an shawo kan matsalar rashin tsaro a wasu sassan jihar.

Sai dai wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa “Kusan mutane 11 da suka hada da ‘yan sanda da mutane bakwai da ke aiki a wurin hakar ma’adinan da farar hula shida ne suka rasa rayukansu a harin.”

Ya ce an kai mutane da dama wadanda suka samu raunuka asibiti kuma suna cikin mawuyacin hali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ChinaHakar Ma'adinaiJami'an TsaroNejaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mataimakin Sufeton ‘Yan Sanda A Ribas

Related

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

8 hours ago
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

9 hours ago
Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja
Manyan Labarai

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

17 hours ago
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

18 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

19 hours ago
Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota

20 hours ago
Next Post
An Yanke Wa Dan Sandan Da Ya Kashe Direban Bas Hukuncin Kisa

'Yan Bindiga Sun Kashe Mataimakin Sufeton 'Yan Sanda A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

July 21, 2025
PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu

PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu

July 21, 2025
Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba

July 21, 2025
Shirin Ba Da Horo A Kasar Sin Ya Taimaka Wa Inganta Masana’antar Gyadar Senegal

Shirin Ba Da Horo A Kasar Sin Ya Taimaka Wa Inganta Masana’antar Gyadar Senegal

July 21, 2025
Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

July 21, 2025
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

July 21, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Hada Sassan Kasa Da Kasa

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Hada Sassan Kasa Da Kasa

July 21, 2025
Adadin Masu Amfani Da Intanet A Sin Ya Kai Sama Da Mutane Biliyan 1.12

Adadin Masu Amfani Da Intanet A Sin Ya Kai Sama Da Mutane Biliyan 1.12

July 21, 2025
Sin Ta Gina Tsarin Layin Dogo Da Manyan Hanyoyin Mota Da Na Aikewa Da Kunshin Sakwanni Mafi Girma A Duniya

Sin Ta Gina Tsarin Layin Dogo Da Manyan Hanyoyin Mota Da Na Aikewa Da Kunshin Sakwanni Mafi Girma A Duniya

July 21, 2025
Sin Ta Yi Tsayin Daka Kan Daidaita Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Siyasa Da Diflomasiyya

Sin Ta Yi Tsayin Daka Kan Daidaita Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Siyasa Da Diflomasiyya

July 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.