• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Tarwatsa Ofishin ‘Yansanda, Sun Kashe ‘Yansanda 3 A Anambra

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Tarwatsa Ofishin ‘Yansanda, Sun Kashe ‘Yansanda 3 A Anambra
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga da suka kai harin bam a ofishin ‘yansanda na Ogidi da ke karamar hukumar Idemili ta Arewa a Jihar Anambra, sun kashe ‘yansanda uku.

LEADERSHIP ta samu labarin cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Asabar.

  • An Gurfanar Da Sojoji 68 A Gaban Kotu Kan Zargin Rashin Da’a A Sokoto
  • Ilimin Taurari Zai Iya Warware Matsalolin Da Kasar Nan Ke Fuskanta –Shaikh Muhajjadina

Majiyoyi a yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun far wa ofishin ‘yansandan inda suka dinga harbi ko ina sannan suka jefa bama-bamai cikin ofishin inda suka kone ginin.

Kakakin ‘yansandan Jihar, DSP Ikenga Tochukwu, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce an tura tawagar ‘yansanda domin dawo da tsaro a yankin.

Ya ce, “Rundunar ‘yansandan Jihar Anambra ta kara karfafa tsaro a yankin Idemili na Arewa da ke jihar, biyo bayan harin da aka kai wa rundunar ‘yansandan yankin Ogidi da sanyin safiyar yau, inda ‘yansanda uku suka rasa rayukansu.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

“Yan bindigar sun fara harbe-harbe kan rundunar ‘yansandan, sannan sun jefa bama-bamai.

DSP Tochukwu ya kara da cewa baya ga ‘yansandan uku da aka kashe, an kone ofishin ‘yansandan.

Ya kara da cewa: “Rundunar ta damu da asarar rayuka da dukiya sakamakon wannan harin.”

Ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankali tare da tabbatar da cewa kwamishinan ‘yansanda, CP Echeng Echeng, ya jajirce wajen hana wadannan miyagu ci gaba da kai hare-hare.

Ya bayyana cewa, CP Echeng ya kara daukar matakai na inganta tsaro da rayuka da dukiyoyi a jihar, inda ya ce tuni aka fara tantance harin da aka kai ofishin ‘yansanda na Ogidi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AnambraKisaMaharaOfishin 'Yansanda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Toni Kroos Ya Kafa Tarihin Cin Kofin Duniya

Next Post

Abin Da Ya Sa Zan Yi Tattaki Daga Neja Zuwa Abuja Idan Atiku Ya Ci – Aminu Hassan

Related

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

37 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

4 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

19 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

20 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

23 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

1 day ago
Next Post
Abin Da Ya Sa Zan Yi Tattaki Daga Neja Zuwa Abuja Idan Atiku Ya Ci – Aminu Hassan

Abin Da Ya Sa Zan Yi Tattaki Daga Neja Zuwa Abuja Idan Atiku Ya Ci - Aminu Hassan

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.