ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Tarwatsa Ofishin ‘Yansanda, Sun Kashe ‘Yansanda 3 A Anambra

by Sadiq
3 years ago
Anambra

Wasu ‘yan bindiga da suka kai harin bam a ofishin ‘yansanda na Ogidi da ke karamar hukumar Idemili ta Arewa a Jihar Anambra, sun kashe ‘yansanda uku.

LEADERSHIP ta samu labarin cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Asabar.

  • An Gurfanar Da Sojoji 68 A Gaban Kotu Kan Zargin Rashin Da’a A Sokoto
  • Ilimin Taurari Zai Iya Warware Matsalolin Da Kasar Nan Ke Fuskanta –Shaikh Muhajjadina

Majiyoyi a yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun far wa ofishin ‘yansandan inda suka dinga harbi ko ina sannan suka jefa bama-bamai cikin ofishin inda suka kone ginin.

ADVERTISEMENT

Kakakin ‘yansandan Jihar, DSP Ikenga Tochukwu, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce an tura tawagar ‘yansanda domin dawo da tsaro a yankin.

Ya ce, “Rundunar ‘yansandan Jihar Anambra ta kara karfafa tsaro a yankin Idemili na Arewa da ke jihar, biyo bayan harin da aka kai wa rundunar ‘yansandan yankin Ogidi da sanyin safiyar yau, inda ‘yansanda uku suka rasa rayukansu.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

“Yan bindigar sun fara harbe-harbe kan rundunar ‘yansandan, sannan sun jefa bama-bamai.

DSP Tochukwu ya kara da cewa baya ga ‘yansandan uku da aka kashe, an kone ofishin ‘yansandan.

Ya kara da cewa: “Rundunar ta damu da asarar rayuka da dukiya sakamakon wannan harin.”

Ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankali tare da tabbatar da cewa kwamishinan ‘yansanda, CP Echeng Echeng, ya jajirce wajen hana wadannan miyagu ci gaba da kai hare-hare.

Ya bayyana cewa, CP Echeng ya kara daukar matakai na inganta tsaro da rayuka da dukiyoyi a jihar, inda ya ce tuni aka fara tantance harin da aka kai ofishin ‘yansanda na Ogidi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka
Manyan Labarai

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda
Manyan Labarai

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Next Post
Abin Da Ya Sa Zan Yi Tattaki Daga Neja Zuwa Abuja Idan Atiku Ya Ci – Aminu Hassan

Abin Da Ya Sa Zan Yi Tattaki Daga Neja Zuwa Abuja Idan Atiku Ya Ci - Aminu Hassan

LABARAI MASU NASABA

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.